Author: Ahmad Habib Ibrahim

Kotun majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland a Kano, ƙarƙashin mai shariʼa Halima Wali ta hana jarumar Kannywood Rashida Adamu Mai Saʼa yin posting a social media har sai an gama shariʼar da Ruƙayya Dawayya ta yi ƙararta kan zargin ɓata suna. Dawayya tana ƙarar Mai Saʼa ne bisa zargin ɓata mata suna da cin mutunci da hana zaman lafiya. An zarge ta da cewa a ranar 15 ga Janairun 2026 ta yi wani bidiyo wanda ta yaɗa a kafafen sada zumunta, inda a ciki ta ci mutuncin Dawayya da cewai wai ta je wajen wani ɗan siyasa ta…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 11 Ga Mayu, 2026 1. Rikicin siyasar jihar Rivers State ya sake ɗaukar sabon salo bayan gwamna Siminalayi Fubara ya bayyana a gaban kwamitin tantancewa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Abuja. Rahotanni sun ce bai shafe fiye da minti 10 ba a wajen tantancewar. 2. Dakarun Nigerian Army sun kama wani da ake zargi ɗan leƙen asiri ne tare da wasu mutane huɗu da suka yi shigar bogi a wasu samame daban-daban da aka gudanar a babban birnin tarayya Abuja. 3. Nigeria Medical Association (NMA) ta tabbatar da sakin likitan da aka sace,…

Read More

Gwamnatin Jihar Borno ta bayyana cewa ta samu gagarumar nasara wajen sake dawo da tsoffin ’yan Boko Haram da iyalansu cikin al’umma, inda sama da mutane 8,000 aka riga aka sake haɗa su da rayuwar jama’a ta hanyar shirin gyaran hali da sake rayuwa. Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta jihar, Zuwaira Gambo, ce ta bayyana hakan a Maiduguri yayin da take bayani kan nasarori da ƙalubalen shirin kawar da tsattsauran ra’ayi da sake haɗa tsoffin mayaƙan cikin al’umma. Ta ce wannan shiri da gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum ke jagoranta, ya samu nasarar kusan kashi 75 cikin…

Read More

Hukumomin lafiya a kalla nahiyoyi hudu na duniya sun fara bincike domin gano duk mutanen da suka yi hulɗa da fasinjojin wani jirgin ruwa da aka samu barkewar cutar Hantavirus a cikinsa. Rahotanni sun bayyana cewa mutane 29 daga kasashe 12 daban-daban sun sauka daga jirgin ruwa mai suna MV Hondius a ranar 24 ga Afrilu bayan an samu bullar cutar. Hantavirus — wata ƙwayar cuta ce mai haɗari da galibi ake kamuwa da ita daga **beraye da wasu rodents Yaya ake kamuwa? Mutum na iya kamuwa idan: * ya shaƙi iska da ta gaurayu da fitsari, bayan gida ko…

Read More

Sabon zargin kisan Dadiyata: Su waye Muhammad Musa da Hassan Gimba? Sabon ikirarin da Muhammad Musa ya yi cewa ya shaida yadda aka kashe Abubakar Idris Dadiyata ya jawo cece-kuce a Najeriya, musamman ganin tarihin rikicinsa da jami’an tsaro. Muhammad Musa, wanda aka taba dangantawa da kwamitin sulhu tsakanin gwamnatin Zamfara da ’yan bindiga, ya kasance cikin wadanda jami’an tsaro suka kama tare da gurfanarwa a kotu bisa zargin ta’addanci, garkuwa da mutane, satar shanu da mallakar makamai. A lokacin kama shi, rundunar ’yan sanda karkashin wani jami’i mai suna Hussaini Hassan Gimba ta fitar da wani bidiyo inda Musa…

Read More

’Yan Najeriya na cikin fargaba yayin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja za ta fara sauraron karar da ta shafi cancantar tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, wajen tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027. Rahotanni sun bayyana cewa ana sa ran Jonathan zai bayyana a kotu da kansa a yau Juma’a domin ci gaba da shari’ar. Wannan na zuwa ne kasa da awanni 24 bayan tsohon shugaban kasar ya nuna sha’awar tsayawa takara a zaben shugaban kasa mai zuwa yayin wani jawabi da ya yi a Abuja ranar Alhamis. Jonathan ya yi wannan furuci ne bayan wasu magoya bayansa…

Read More

Tsohon Shugaban Kasa, Goodluck Jonathan, ya bayyana cewa zai fara tuntuba da mutane daban-daban kan yiwuwar shiga zaben shugaban kasa na shekarar 2027. Jonathan ya bayyana hakan ne ranar Alhamis a Abuja bayan wasu magoya bayansa sun gudanar da tattaki zuwa ofishinsa suna rokon sa ya tsaya takara a zaben shugaban kasa mai zuwa. A jawabin nasa, Jonathan ya jaddada muhimmancin kishin kasa da zaman lafiya, yana cewa: “Abu mafi muhimmanci da Najeriya ke bukata shi ne zaman lafiya. Matasa dole su ci gaba da neman sahihin zabe mai cike da gaskiya da adalci.” Ya kuma kara da cewa zaben…

Read More