Blog

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 28, Afrilu. 2026

    Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 28, Afrilu. 2026

    Labaran Najeriya Na Yau – 28 Ga Afrilu, 2026

    1. Gabanin zaɓen 2027, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen da ya gabata, Peter Obi, tare da wasu shugabannin Kudu maso Gabas, sun gana da tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan. An gudanar da ganawar ne a ɓoye a gidansa da ke Abuja a daren Litinin.

    2. Jam’iyyar Labour Party za ta gudanar da babban taronta na ƙasa a yau ƙarƙashin jagorancin kwamitin rikon ƙwarya da Sanata Nenadi Usman ke jagoranta, yayin da ake fama da rikicin shugabanci tsakanin ɓangarorin jam’iyyar. Za a gudanar da taron a Umuahia, Jihar Abia, inda ake sa ran wakilai daga sassa daban-daban za su halarta domin tattauna muhimman batutuwa da suka haɗa da tsarin shugabanci da makomar jam’iyyar.

    3. Gwamnan Jihar Lagos, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana goyon bayansa ga mataimakinsa, Obafemi Hamzat, a matsayin wanda yake so ya gaje shi a zaɓen gwamna na 2027. Ya bayyana hakan ne bayan wata ganawa ta sirri da aka yi a Lagos House, Marina.

    4. Kotun soja da ke shari’ar yunƙurin juyin mulki da aka dakile a bara za ta ci gaba da zaman ta a ranar 8 ga Mayu, kamar yadda mai magana da yawun hedikwatar tsaro ya bayyana. Kimanin jami’an soja talatin da shida ne ake tuhuma da shirin kifar da gwamnati.

    5. Ofishin jakadancin Najeriya a Johannesburg ya tabbatar da kashe wasu ‘yan Najeriya biyu a Afirka ta Kudusakamakon ƙaruwar rikicin kyamar baki. An bayyana sunayensu da Amaramiro Emmanuel da Ekpenyong Andrew. Jakada Ninikanwa Okey-Uche ya ce Emmanuel ya mutu ne sakamakon raunukan da ya samu bayan dukan da ake zargin sojojin Afirka ta Kudu suka yi masa.

    6. An shiga firgici a yankin Igando na Jihar Lagos bayan zargin cewa wasu ma’aurata, Paul Onyeama da Adline Ogbonna, sun doke ‘yarsu ta raino mai shekaru 10 har ta mutu. Rahotanni sun nuna cewa sun dade suna azabtar da yarinyar da duka da kuma wahalar da ita da ayyuka masu nauyi.

    7. Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a ƙauyen Imafon da ke ƙaramar hukumar Akure North ta Jihar Ondo, inda suka sace manajan gona, Afolabi Ajayi. An ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:30 na safe yayin da yake shiga gonar kaji.

    8. Rundunar NDLEA a Jihar Edo ta ce ta kama magungunan da aka hana amfani da su, ciki har da tramadol mai nauyin kilo 748.02, a kan titin Benin zuwa Lagos. Kwamandan NDLEA na jihar, Mitchell Ofoyeju, ya bayyana hakan ga manema labarai.

    9. Shugabancin jam’iyyar Accord Party na ƙasa ya nesanta kansa daga rahotannin da ke haɗa ta da wani shirin haɗin gwiwar jam’iyyun adawa domin fitar da ɗan takara guda a zaɓen 2027. Kakakin jam’iyyar, Joseph Omorogbe, ya ce wannan rahoto ba gaskiya ba ne kuma yana yaudarar jama’a.

    10. Hukumar Zaɓe mai zaman kanta (INEC) a Jihar Rivers ta bayyana cewa ta shirya fara aikin karɓar ƙorafe-ƙorafe da gyare-gyare a mataki na biyu na rajistar masu kaɗa ƙuri’a (CVR). Kwamishinan zaɓe na jihar, Farfesa Gabriel Yomere, ne ya bayyana hakan ta bakin jami’ar hulɗa da jama’a, Geraldine Ekelemu.

  • AREWA24 TA NA NEMAN DIYAR NAIRA BILIYAN GOMA KAN BATA SUNA

    AREWA24 TA NA NEMAN DIYAR NAIRA BILIYAN GOMA KAN BATA SUNA

    AREWA24, tashar talabijin da ke kan gaba wajen yaɗa shirye-shirye masu nishaɗantar da iyali da tsarin rayuwa cikin harshen Hausa, wadda ke da ofishin samar da shirye-shirye a Najeriya da yammacin Afirka, ta shigar da ƙarar neman diyar naira biliyan goma, bisa zargin ɓata suna a kan Alhaji Ahmed Tijjani Ramalan, da kamfanin Atar Communications Nigeria Limited (masu gudanar da Liberty TV da Radio), da kuma Ƙungiyar Masu Kafofin Yaɗa Labarai na Arewa (NBMOA), biyo bayan wasu jerin zarge-zarge na karya, masu illa, kuma marasa tushe da aka yi wa kamfanin.

    Matakin na shari’a, wanda aka shigar a gaban Babban Kotun Jiha da ke Jalingo, na neman a biya diyya kan taɓa martabar kamfanin da kuma asarar kuɗi da ya tafka sakamakon kalaman da ake zargin Ƙungiyar Masu Kafofin Yaɗa Labarai na Arewa (NBMOA), da Tijjani Ramalan sun fitar, waɗanda AREWA24 ta tabbatar cewa kalamai ne na yaudara, kuma suna da illa ga kimar da aka san kamfanin da ita, da kuma ayyukansu. Kamfanin ya jaddada cewa wadannan maganganu ba su da wani tushe na gaskiya, kuma akwai yiwuwar su lalata aminci da yarda da kamfanin ya gina tsakaninsa da masu kallon tashar, da abokan hulda, da masu ruwa da tsaki tsawon shekaru.

    A cikin wani jawabi da ya fitar, kamfanin AREWA24 ya jaddada kudirinsa na kiyaye matakai na ƙwarewa, gaskiya, da shirye-shirye masu nagarta. “Mun gina martabarmu ne bisa shirye-shiryen nishadi masu inganci, wadanda suka dace da al’adu kuma suke da tasiri ga miliyoyin masu kallo a Najeriya, da yammacin Nahiyar Afirka da ma sauran sassa na duniya. Ba za mu taɓa barin duk wasu zarge-zarge marasa tushe daga wasu “gurbatattun” mutane su lalata yarda da kyakkyawar alaƙar da muka kafa ba,” in ji kamfanin.

    AREWA24 ta ƙara da cewa, yayin da take maraba da sukar da za ta kawo ci gaba, za ta dauki dukkan matakan shari’a da suka dace don kare mutuncinta, ma’aikatanta, da muradun kasuwancinta. Kamfanin ya nuna kwarin gwuiwa kan tsarin shari’a sannan ya sake jaddada jajircewarsa a kan nuna gaskiya da amana.
    Baya ga sauran bukatu, ƙarar na neman a biya diyar kudi har naira biliyan goma, da janye kalaman bata suna da aka yi a bainar jama’a, da kuma bayar da hakuri a hukumance daga Ahmed Tijjani Ramalan, da Atar Communications Nigeria Limited da kuma ƙungiyar NBMOA.

    AREWA24 na ci gaba da gudanar da ayyukanta a matsayin daya daga cikin manyan kafafen yada labarai na talabijin da samar da shirye-shirye a yankin Sahara na Afirka, da yaɗa ingantattun shirye-shirye masu nishaɗantarwa da ilimantarwa da aka tsara musamman domin ɗimbin masu kallonta daga bangarori daban-daban.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 27, Afrilu. 2026

    Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 27, Afrilu. 2026

    Labaran Najeriya Na Yau – 27 Ga Afrilu, 2026

    1. An shiga yanayi na tashin hankali da rashin natsuwa a Jihar Kano a ranar Litinin, bayan da Gwamna Abba Yusuf ya sauya sheƙa daga jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) zuwa jam’iyya mai mulki ta All Progressives Congress (APC). An sake tsara ranar sauya shekar zuwa Litinin bayan an fara ɗora ta a ranar 5 ga Janairu. Duk da cewa babu jawabi na hukuma ko bikin bayyana sauya shekar, a bayyane yake cewa gwamnan da gwamnatinsa sun daina kasancewa a ƙarƙashin tutar NNPP.
    2. Jimillar ’ya’yan sarauta 95 maza da mata daga Gidan Sarautar Fusengbuwa sun nuna sha’awar neman gadon sarautar Awujale na Ijebuland. Shugaban gidan sarautar (Olori Ebi) na Fusengbuwa, wanda kuma ake kira Otunba Jadiara, Lateef Owoyemi, ne ya bayyana hakan a yau yayin fara taron karɓar sunayen masu nema da aka gudanar a Bisi Rodipe Hall, GRA, Ijebu Ode.
    3. Mutane sama da 50 da suka halarci zanga-zangar da aka yi a ranar Asabar da ta gabata a Ekpoma, ƙaramar hukumar Esan West, an kama su. An kama waɗanda ake zargin a wurare daban-daban a Ekpoma. A yayin zanga-zangar, an wawashe shaguna da dama tare da lalata fadar Onojie na Ekpoma.
    4. Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya umurci dukkan masu kula da rajistar mambobin jam’iyyar a jihohi da su tabbatar da cewa an yi wa kowane memba rajista a cikin shirin rajistar lantarki da ke gudana a faɗin ƙasa. Ya kuma yi gargaɗin cewa gazawa wajen aiwatar da wannan nauyi na iya janyo musu rasa muƙamansu.
    5. Tsohon Babban Hafsan Sojin ƘasaTukur Buratai, ya ce yawaitar amfani da sojojin Najeriya wajen tsaron cikin gida na raunana ƙarfin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya da sauran hukumomin tsaro na farar hula. A cewarsa, yaɗuwar sojoji a jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya na rage bunƙasa da ingancin aikin ’yan sanda.
    6. An tsinci mambobin iyali shida sun mutu a gidansu da ke ƙauyen Ogale Eleme a Ƙaramar Hukumar Eleme ta Jihar Rivers. An gano gawarwakin ne a ranar Lahadi bayan jami’an ’yan sanda sun fasa ƙofar gidan da misalin ƙarfe 3 na rana. Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Grace Iringe-Koko, ta ce binciken farko ya nuna cewa mai yiyuwa mutuwar ta faru ne sakamakon hayakin janareta.
    7. Fasto Chris Okafor, Babban Fasto na cocin Mountain of Liberation and Miracles Ministries, ya amsa gayyatar ’yan sanda a Jihar Legas dangane da zarge-zarge da dama da ake masa. Majiyoyi sun ce faston ya halarci gayyatar kuma an yi masa tambayoyi na tsawon awanni a sashen binciken manyan laifuka na jihar da ke Panti Street, Yaba, Lagos.
    8. ’Yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun nemi kuɗin fansa Naira miliyan 100 domin sakin mutane takwas ’yan asalin Imoga da aka sace a daren Juma’a. Sarkin Imoga, Oba Patrick Obajoye (Okpahi na Masarautar Imoga), ya bayyana hakan a ranar Litinin ta wayar tarho, inda ya ce an sace mutanen ne a Star Boy Hotel da ke kan hanyar Imoga–Ibillo a Arewa ta Jihar Edo.
    9. Wasu da ake zargin ’yan daba (cultists) ne sun harbe wani mutum mai suna Tyohee Aseer har lahira a yankin Wurukum da ke Makurdi, Jihar Benue. An ce lamarin ya faru ne a daren Lahadi, mako guda kacal bayan kashe-kashe masu yawa sakamakon rikicin ƙungiyoyin daba a jihar. Shugaban Ƙaramar Hukumar Makurdi, Joseph Keffi, ya yi Allah-wadai da kisan ta bakin mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Teran Nathaniel.
    10. Tsohon Gwamnan Jihar Imo, Rt. Hon. Emeka Ihedioha, ya shiga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a hukumance. Ihedioha ya kammala rajistarsa a ranar Litinin, 12 ga Janairu, 2026, a Mbutu Ward da ke Ƙaramar Hukumar Aboh-Mbaise ta Jihar Imo, inda aka ba shi katin membobinsa na ADC mai lamba 001.
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 23, Afrilu. 2026

    Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 23, Afrilu. 2026

    Labaran Najeriya Na Yau – 23 Ga Afrilu, 2026

    1. Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya ajiye mukaminsa domin neman tsayawa takarar gwamna a Jihar Oyo. Wasikar murabus ɗinsa ta kawo ƙarshen jita-jitar da ke yawo, musamman bayan ya wuce wa’adin ranar 31 ga Maris da Shugaba Bola Tinubu ya bai wa masu rike da mukaman siyasa su yi murabus idan za su tsaya takara.

    2. Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa tsohon Ministan Kudi, Wale Edun, da tsohon Ministan Gidaje, Ahmed Musa Dangiwa, sun yi murabus da kansu daga Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC), ba wai an kore su ba. Mai magana da yawun Shugaba Tinubu, Bayo Onanuga, ya ce Edun ya yi murabus ne saboda dalilan lafiya.

    3. Jakadan Najeriya da aka naɗa zuwa ƙasar Algeria, Mohammed Mahmud Lele, ya rasu bayan fama da jinya mai tsawo. Yana da shekaru 50, kuma ya rasu a birnin Ankara na ƙasar Turkiyya inda yake karɓar magani. Ma’aikatar Harkokin Waje ta ce ya rasu ne da sanyin safiyar ranar 19 ga Afrilu.

    4. Gwamnatin Jihar Cross River ta ce ta gano tare da ware mutane 10 da suka yi mu’amala da ɗan ƙasar China da ya sake shigo da cutar COVID-19 cikin Najeriya. Likitan kula da cututtuka na jihar, Dr. Inyang Ekpenyong, ya ce an gano su ne ta hanyar binciken wadanda suka yi hulɗa da marar lafiyar.

    5. Kotun Koli ta ajiye hukunci kan ƙorafe-ƙorafe da suka taso daga rikicin cikin gida na jam’iyyar PDP, bayan ta saurari dukkan ɓangarori. Wannan shari’a ta riga ta kawo sauye-sauye a shugabancin jam’iyyar, inda aka soke babban taron Ibadan tare da tabbatar da dakatar da wasu manyan jami’ai.

    6. Shugaba Bola Tinubu ya gana da tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. An gudanar da ganawar ne a ɓoye, kuma ana zaton tana daga cikin tattaunawa da suke yi akai-akai kan al’amuran siyasa na Yammacin Afirka da kuma hulɗar Najeriya da nahiyar.

    7. Mutane shida da ake tuhuma sun musanta laifuka guda 13 da suka shafi zargin ta’addanci da shirya juyin mulki a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. An gurfanar da su a ƙarƙashin shari’a mai lamba FHC/ABJ/CR/206/2026, inda Babban Lauyan Tarayya, Lateef Fagbemi (SAN), da Daraktan tuhumar jama’a, Rotimi Oyedepo (SAN), ke jagorantar ƙara.

    8. Majalisar Dattawa ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta yi la’akari da ɗaukar matakan gaggawa, ciki har da yiwuwar dakatar da harkokin siyasa a wasu jihohi takwas da ke fuskantar matsalar tsaro. Wannan kira ya biyo bayan damuwar da ke ƙaruwa a Majalisar kan sake ɓarkewar hare-haren ‘yan tada kayar baya, bayan da Sanata Abdul Ningi ya gabatar da batun a zaman majalisa.

    9. Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirin yafewa kamfanonin jiragen sama na cikin gida bashin da suke bin hukumomin sufurin jiragen sama, domin rage tasirin tsadar man jirgi (Jet A1). Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya bayyana hakan a wani taro a Abuja domin magance hauhawar farashin man jirgi.

    10. Majalisar Dokokin Jihar Kano ta shirya ranar Litinin domin tantance Murtala Garo, bayan da Gwamna Abba Yusufya naɗa shi a matsayin Mataimakin Gwamna. Kakakin majalisar, ta bakin mai magana da yawunsa Kamaludden Shawai, ne ya bayyana hakan.


  • Mazauna Lagos Sun Rika Debar Mai Bayan Tankar Ta Kife a Gadarin Tincan

    Mazauna Lagos Sun Rika Debar Mai Bayan Tankar Ta Kife a Gadarin Tincan

    Wata tankar man fetur (PMS) ta kife a Gadar Tincan Liverpool da ke Apapa, Jihar Lagos, lamarin da ya janyo mutane suka rika debar man da ya zube daga karkashin gadar.

    Tashar Channels Television ta wallafa bidiyon faruwar lamarin a safiyar ranar Litinin, inda aka ga wasu ‘yan Najeriya na kwasar man fetur daga tankar da ta kife, duk da hadarin da ke tattare da hakan.

    A cewar rahoton Channels TV:

    “Abin da ke faruwa a yanzu a Gadar Tincan Liverpool, Apapa: Tankar mai ta kife, mutane kuma suna dibar man da ya zube daga karkashin gadar.”

    Jaridar DAILY POST ta bayyana cewa fashewar tankokin mai na ci gaba da zama babbar masifa a Najeriya, duk da gargadin da hukumomi ke ta yi akai-akai game da hadarin tattara man da ya zube, wanda kan haddasa asarar rayuka da dukiyoyi.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 13, Janairu. 2026

    Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 13, Janairu. 2026

    Labaran Najeriya Na Yau – 13 Ga Junairu, 2026

    1. An shiga yanayi na tashin hankali da rashin natsuwa a Jihar Kano a ranar Litinin, bayan da Gwamna Abba Yusuf ya sauya sheƙa daga jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) zuwa jam’iyya mai mulki ta All Progressives Congress (APC). An sake tsara ranar sauya shekar zuwa Litinin bayan an fara ɗora ta a ranar 5 ga Janairu. Duk da cewa babu jawabi na hukuma ko bikin bayyana sauya shekar, a bayyane yake cewa gwamnan da gwamnatinsa sun daina kasancewa a ƙarƙashin tutar NNPP.
    2. Jimillar ’ya’yan sarauta 95 maza da mata daga Gidan Sarautar Fusengbuwa sun nuna sha’awar neman gadon sarautar Awujale na Ijebuland. Shugaban gidan sarautar (Olori Ebi) na Fusengbuwa, wanda kuma ake kira Otunba Jadiara, Lateef Owoyemi, ne ya bayyana hakan a yau yayin fara taron karɓar sunayen masu nema da aka gudanar a Bisi Rodipe Hall, GRA, Ijebu Ode.
    3. Mutane sama da 50 da suka halarci zanga-zangar da aka yi a ranar Asabar da ta gabata a Ekpoma, ƙaramar hukumar Esan West, an kama su. An kama waɗanda ake zargin a wurare daban-daban a Ekpoma. A yayin zanga-zangar, an wawashe shaguna da dama tare da lalata fadar Onojie na Ekpoma.
    4. Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya umurci dukkan masu kula da rajistar mambobin jam’iyyar a jihohi da su tabbatar da cewa an yi wa kowane memba rajista a cikin shirin rajistar lantarki da ke gudana a faɗin ƙasa. Ya kuma yi gargaɗin cewa gazawa wajen aiwatar da wannan nauyi na iya janyo musu rasa muƙamansu.
    5. Tsohon Babban Hafsan Sojin ƘasaTukur Buratai, ya ce yawaitar amfani da sojojin Najeriya wajen tsaron cikin gida na raunana ƙarfin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya da sauran hukumomin tsaro na farar hula. A cewarsa, yaɗuwar sojoji a jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya na rage bunƙasa da ingancin aikin ’yan sanda.
    6. An tsinci mambobin iyali shida sun mutu a gidansu da ke ƙauyen Ogale Eleme a Ƙaramar Hukumar Eleme ta Jihar Rivers. An gano gawarwakin ne a ranar Lahadi bayan jami’an ’yan sanda sun fasa ƙofar gidan da misalin ƙarfe 3 na rana. Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Grace Iringe-Koko, ta ce binciken farko ya nuna cewa mai yiyuwa mutuwar ta faru ne sakamakon hayakin janareta.
    7. Fasto Chris Okafor, Babban Fasto na cocin Mountain of Liberation and Miracles Ministries, ya amsa gayyatar ’yan sanda a Jihar Legas dangane da zarge-zarge da dama da ake masa. Majiyoyi sun ce faston ya halarci gayyatar kuma an yi masa tambayoyi na tsawon awanni a sashen binciken manyan laifuka na jihar da ke Panti Street, Yaba, Lagos.
    8. ’Yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun nemi kuɗin fansa Naira miliyan 100 domin sakin mutane takwas ’yan asalin Imoga da aka sace a daren Juma’a. Sarkin Imoga, Oba Patrick Obajoye (Okpahi na Masarautar Imoga), ya bayyana hakan a ranar Litinin ta wayar tarho, inda ya ce an sace mutanen ne a Star Boy Hotel da ke kan hanyar Imoga–Ibillo a Arewa ta Jihar Edo.
    9. Wasu da ake zargin ’yan daba (cultists) ne sun harbe wani mutum mai suna Tyohee Aseer har lahira a yankin Wurukum da ke Makurdi, Jihar Benue. An ce lamarin ya faru ne a daren Lahadi, mako guda kacal bayan kashe-kashe masu yawa sakamakon rikicin ƙungiyoyin daba a jihar. Shugaban Ƙaramar Hukumar Makurdi, Joseph Keffi, ya yi Allah-wadai da kisan ta bakin mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Teran Nathaniel.
    10. Tsohon Gwamnan Jihar Imo, Rt. Hon. Emeka Ihedioha, ya shiga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a hukumance. Ihedioha ya kammala rajistarsa a ranar Litinin, 12 ga Janairu, 2026, a Mbutu Ward da ke Ƙaramar Hukumar Aboh-Mbaise ta Jihar Imo, inda aka ba shi katin membobinsa na ADC mai lamba 001.
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 12, Janairu. 2026

    Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 12, Janairu. 2026

    Labaran Najeriya Na Yau – 12 Ga Junairu, 2026

    1. Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na Ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a daren Lahadi domin halartar taron Abu Dhabi Sustainability Week 2026 (ADSW 2026), wani taron duniya da ke mayar da hankali kan ci gaban dorewa. Shugaban ƙasar ya isa birnin da misalin ƙarfe 11:30 na dare agogon wurin, inda Karamin Ministan Harkokin Waje, Sheikh Shakhboot Nahyan Al Nahyan, ya tarbe shi.
    2. Kungiyar Likitocin Gidajen Asibiti (NARD) ta dakatar da yajin aikin da ta shirya yi a faɗin ƙasar, bayan da ta ce an samu gagarumin ci gaba kan buƙatunta ta hanyar tattaunawa da Gwamnatin Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki. An yanke wannan shawara ne a taron gaggawa na majalisar zartarwa ta ƙasa da aka yi ta yanar gizo.
    3. Wata babbar gobara ta tashi a Ogun Free Trade Zone da ke Igbesa a Jihar Ogun, inda ta lalata wata masana’anta tare da yaɗuwa zuwa gidajen zama da ke kusa. Rahotanni sun ce gobarar ta fara ne da tsakar dare kuma ta ci gaba har zuwa safiyar Lahadi kafin jami’an agaji su samu shawo kanta.
    4. Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya mayar da martani ga masu kiran a tsige shi, inda ya ce hakan na cikin ikon Shugaba Bola Tinubu idan ya ga dama. Wike ya faɗi haka ne a Lahadi yayin ziyarar “na gode” da ya kai ƙaramar hukumarsa ta Obio-Akpor a Jihar Rivers, yana jaddada cewa tun 1999 mutanen yankin ba su taɓa ba shi kunya ba.
    5. Majalisar Dokokin Jihar Rivers ta yi gargaɗi kan abin da ta kira shiri na wasu mutane da ke da alaƙa da bangaren zartarwa na neman umarnin kotu domin hana majalisar gudanar da ayyukanta. A cikin wata sanarwa a Lahadi, Shugaban Kwamitin Yada Labarai da Korafe-korafe na Majalisar, Dr. Enemi Alabo George, ya ce ana shirin samun umarnin ex parte daga wata babbar kotu a jihar da ke aiki a wajen Port Harcourt.
    6. Gwamnan Jihar Rivers, Sir Siminalayi Fubara, ya ce abin da jihar ke buƙata a halin yanzu shi ne zaman lafiya, yana mai yin ishara ga masu sukar sa da cewa “karnuka na haushi ne idan ba su fahimta ba.” Fubara ya faɗi hakan ne a Cocin St. Cyprian’s Anglican da ke Port Harcourt yayin taron addu’ar coci na haɗin dariku don tunawa da Ranar Tunawa da Sojoji ta 2026.
    7. Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya ce Najeriya na fuskantar jarabawa sakamakon tarin ƙalubalen tsaro da ke ƙasar, amma ya tabbatar da cewa ƙasar za ta yi nasara. A lokaci guda, wani limami, Most Rev. Uche Dan Okafor, ya roƙi sojojin Najeriya da kada su yi tunanin kifar da gwamnati ta dimokiraɗiyya kamar yadda ake gani a wasu ƙasashen Yammacin Afirka.
    8. ’Yan bindiga da ake zargin makiyaya masu makami ne sun kashe wani soja da jami’in NSCDC a ƙauyen Udeku da ke gundumar Turan a Ƙaramar Hukumar Kwande ta Jihar Benue. Wani jagoran al’umma, Lawrence Akerigba, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce harin ya tilasta wa jama’a da dama guduwa daga yankin.
    9. Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kogi ta ce an kashe ’yan bindiga da dama tare da tarwatsa hanyoyin sadarwarsu a wani sabon aikin tsaro, kodayake ba a bayyana inda aka gudanar da aikin ba. Kakakin rundunar, William Aya, ya ce nasarar ta samu ne a wani haɗin gwiwar aiki tsakanin ’yan sanda da sojoji, tare da taimakon sashen jiragen sama na ’yan sanda.
    10. Rundunar ’Yan Sandan Jihar Sokoto ta tabbatar da cewa an kashe ’yan canjin kuɗi biyu yayin da ake zargin ’yan bindiga sun kai hari kasuwar canjin kuɗi ta Durusar Gawo da ke gundumar Kurdula a Ƙaramar Hukumar Gudu. Kakakin rundunar, DSP Ahmad Rufa’i, ya ce maharan sun iso da tsakar rana a Lahadi, suka buɗe wuta kan ’yan kasuwa, inda mutum ɗaya ya mutu nan take, ɗayan kuma ya rasu daga baya a Asibitin Dogon Dutse.