Author: Ahmad Habib Ibrahim

1. Makinde ya ce a shirye yake ya sadaukar da kansa domin ceto ɗaliban OyoGwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayyana cewa a shirye yake ya yi duk abin da ya dace domin tabbatar da sakin ɗalibai da malamai 46 da aka sace a ƙaramar hukumar Oriire. Ya kuma tabbatar da cewa Oyo ba za ta fuskanci irin abin da ya faru da ‘yan matan Chibok ba. 2. Kotun Ɗaukaka Ƙara ta dakatar da soke rijistar ADCKotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta dakatar da aiwatar da hukuncin da ya umarci INEC ta soke rijistar jam’iyyar ADC da wasu jam’iyyu…

Read More

Takaitattun Labaran Najeriya na Yau 1. Majalisar Wakilai za ta kada kuri’a kan kafa ‘yan sandan jihohiMajalisar Wakilai ta bayyana cewa za ta yi kuri’a kan gyaran kundin tsarin mulki domin bai wa jihohi da ƙananan hukumomi damar kafa nasu rundunar ‘yan sanda, a matsayin wata hanya ta magance matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara a ƙasar. 2. Gobara ta tayar da hankula a Majalisar DattawaWata gobara da ta tashi daga wani sashe na girki a ginin Majalisar Dattawa da ke Abuja ta haddasa firgici, inda sanatoci, ma’aikata da baƙi suka yi gaggawar ficewa kafin aka shawo kan lamarin. 3.…

Read More

Takaitattun Labaran Najeriya na Yau 1. Sunday Igboho Ya Yi Barazanar Fitar da Sunayen Masu Daukar Nauyin Garkuwa da Dalibai Jagoran masu fafutukar kafa kasar Yarbawa, Sunday Igboho, ya yi barazanar bayyana sunayen wasu ‘yan siyasa da yake zargi da daukar nauyin masu garkuwa da daliban da aka sace a karamar hukumar Oriire ta jihar Oyo. Ya bayyana hakan ne yayin ganawa da sabbin shugabannin kungiyar daliban Najeriya (NANS) a gidansa da ke Ibadan. 2. Shirin Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Ya Kai Wani Muhimmin Mataki Akwai alamun cewa an kusa cimma nasarar kafa rundunar ‘yan sandan jihohi a Najeriya domin…

Read More

1. Majalisar Dattawa ta sake yin Allah-wadai da sace ɗalibai a Oyo Majalisar Dattawa ta yi tir da sace ɗalibai, malamai da wani ƙaramin yaro a ƙaramar hukumar Oriire ta Jihar Oyo. Ta bayyana lamarin a matsayin hari ga makomar Najeriya tare da kira da a ceto duk waɗanda har yanzu suke hannun masu garkuwa da mutane. 2. Kotu ta yanke wa mutum huɗu hukuncin kisa kan harin cocin Owo Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa mutum huɗu hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda hannu a harin da aka kai Cocin St. Francis da ke Owo, Jihar…

Read More

1. Akpabio ya yi alƙawarin taimaka wa sanatocin da suka faɗi zaɓen fidda gwani** Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce majalisar na ƙoƙarin nemo wa wasu sanatocin da suka gaza samun tikitin takarar zaɓen 2027 wasu damar siyasa masu kyau. 2. ‘Yan bindiga sun sake kai hari a Sokoto ‘Yan bindiga sun sake afkawa ƙauyen Dan Gulbi da ke ƙaramar hukumar Tureta a Jihar Sokoto, kwanaki biyu kacal bayan wani hari makamancin haka ya kashe mutum 17. Maharan sun shiga ƙauyen da babura suna harbe-harbe, lamarin da ya tilasta wa mazauna guduwa. 3. INEC ta yi bayani kan takaddamar…

Read More

Takaitattun Labaran Najeriya na Yau – Talata, 2 Yuni 2026 1. Tinubu Ya Yabi Rundunar Sojin Ruwa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce Rundunar Sojin Ruwan Najeriya (Navy) ta zama ginshiƙi wajen kare dukiyoyin ruwa da bunƙasa tattalin arzikin ƙasa. Ya yabawa rundunar bisa rawar da take takawa wajen ƙara kudaden shiga na gwamnati. 2. Babachir Lawal Ya Soki Atiku Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya caccaki Atiku Abubakar, yana mai cewa bai dace ya zama shugaban ƙasa ba. Ya kuma yi zargin cewa an yi maguɗi a zaɓen fidda gwanin ADC domin Atiku ya samu tikitin takara. 3.…

Read More

MAGANAR GASKIYA DANGANE DA FIM ƊIN “ABADAN” Daga: Ahmad Habib Ibrahim (Films Editor) Bayan kallon fim ɗin ABADAN, akwai abubuwa masu yawa da suka burge ni, haka kuma akwai wasu wuraren da nake ganin da za a iya ƙara gyara domin aikin ya fi ƙarfi. Da farko, ina ganin rawar da aka bai wa babban jarumin ba ita ce rawar da ta fi dacewa da shi ba. A ganina, irin wannan role ɗin ya fi dacewa da Adam A. Zango. Duk da haka, jarumin ya yi ƙoƙari sosai wajen fassara halayen da aka ɗora masa. Game da labarin fim ɗin…

Read More