Kungiyar masu gidajen sayar da man fetur ta Najeriya (PETROAN) ta yi gargadin cewa ‘yan Najeriya na iya fara sayen fetur (PMS), dizal (AGO) da sauran kayayyakin mai da dalar Amurka (US Dollar) idan har Gwamnatin Tarayya ba ta dawo da tsarin Naira-for-Crude da Matatar Dangote ba. Shugaban PETROAN na ƙasa, Billy Gillis-Harry, ne ya bayyana hakan a wata hira da DAILY POST a ƙarshen mako. A makon da ya gabata ne Matatar Dangote ta koma karɓar dalar Amurka wajen sayar da kayayyakin man da take tacewa. Wannan mataki ya nuna dakatar da tsarin Naira-for-Crude, wanda ke bai wa dillalan…
Author: Ahmad Habib Ibrahim
1. Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin ƙwace kadarori 48 da ake dangantawa da tsohon Ministan Shari’a kuma tsohon Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Malami (SAN), ta mika su ga Gwamnatin Tarayya. Hukuncin ya biyo bayan bukatar da EFCC ta gabatar. 2. Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA) ta haramta wa matukin jirgin Amurka da ya shiga hatsarin jirgi a filin jirgin saman Asaba ranar 10 ga Yuni yin aiki a sararin samaniyar Najeriya. Haka kuma ta dakatar da mataimakin matukin jirgin har sai an kammala bincike. 3. Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS)…
1. An kama Adeniyi Adeyemi, Darakta Janar na kungiyar PFIPC, bayan kotu ta ba da umarnin cafke shi saboda rashin halartar shari’arsa. 2. Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bukaci Majalisar Wakilai ta gyara Kundin Tsarin Mulki domin ba wa jihohi damar kafa ‘yan sandan jiha (State Police) don inganta tsaro. 3. Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa Muhammad Sani hukuncin daurin shekaru 20, bayan samunsa da laifin boye bayanan wani fitaccen dan bindiga mai suna Danranmi. 4. Rundunar ‘yan sandan Legas ta bankado wata kungiyar damfara da ake zargi da satar motocin alfarma ta hanyar yaudara, inda…
Tsohon Ministan Ƙirƙire-ƙirƙire, Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji, ya musanta zargin da ake masa na ƙirƙirar takardar shaidar digirinsa da kuma takardar kammala aikin bautar ƙasa (NYSC) bayan gwamnatin tarayya ta gurfanar da shi a kotu. Hukumar ICPC (Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission) ce ta shigar da ƙarar, kuma an gurfanar da shi a gaban Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. Ana tuhumar Nnaji da laifuffuka guda shida, ciki har da zargin ƙirƙirar takardar digiri daga Jami’ar Najeriya da ke Nsukka (UNN) da kuma takardar kammala bautar ƙasa ta NYSC, waɗanda ya…
Gwamnatin Tarayya ta dakatar da shirin ƙara kuɗin rajistar jarabawar WAEC (WASSCE) da NECO (SSCE), bayan suka da korafe-korafen da suka biyo bayan sanarwar ƙarin kuɗin. Sanarwar dakatarwar na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktar Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a ta Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Boriowo Folasade, ta fitar a ranar Litinin. A cewar gwamnatin, an janye wasiƙar da aka fitar ranar 18 ga Yuni, 2026, wadda ta sanar da ƙarin kuɗin rajistar WAEC da NECO. Ma’aikatar ta bayyana cewa an dakatar da shirin ne domin ba da damar sake nazari da kuma tattaunawa da masu ruwa da…
Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya (FCT) da ke zamanta a Maitama, Abuja, ta bayar da umarnin tsare tsohon Shugaban Kotun Da’a ta Kasa (Code of Conduct Tribunal – CCT), Danladi Umar, a Gidan Gyaran Hali na Kujebayan gwamnatin tarayya ta gurfanar da shi kan tuhume-tuhume guda huɗu da suka shafi zargin cin hanci da rashawa da kuma amfani da mukami ba bisa ƙa’ida ba. Mai shari’a Peter Kekemeke ne ya bayar da umarnin tsare Umar bayan ya musanta dukkan tuhume-tuhumen da ake yi masa. Gwamnatin Tarayya ta zarge shi da karɓar kuɗaɗen cin hanci daga ‘yan kwangila yayin da yake…
Rahoton WFP kan matsananciyar yunwa a Arewacin Najeriya ya tayar da hankula Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ta yi gargadin cewa Arewacin Najeriya na fuskantar babbar barazanar yunwa idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba. A cewar rahoton da hukumar ta fitar a makon da ya gabata, rikice-rikicen tsaro da ƙarancin tallafin jin ƙai sun sa yankin ke fuskantar mafi munin matsalar yunwa cikin kusan shekaru goma. Hukumar ta ce miliyoyin mutane na fama da matsananciyar rashin abinci, tare da kira ga ƙasashen duniya da su bayar da tallafin kuɗi cikin gaggawa domin hana lamarin ƙara ta’azzara. Rahoton…