Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Ana cikin fargaba yayin da kotu za ta fara sauraron karar cancantar Jonathan

Ana cikin fargaba yayin da kotu za ta fara sauraron karar cancantar Jonathan

By Ahmad Habib IbrahimMay 8, 2026No Comments1 Min Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

’Yan Najeriya na cikin fargaba yayin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja za ta fara sauraron karar da ta shafi cancantar tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, wajen tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027.

Rahotanni sun bayyana cewa ana sa ran Jonathan zai bayyana a kotu da kansa a yau Juma’a domin ci gaba da shari’ar.

Wannan na zuwa ne kasa da awanni 24 bayan tsohon shugaban kasar ya nuna sha’awar tsayawa takara a zaben shugaban kasa mai zuwa yayin wani jawabi da ya yi a Abuja ranar Alhamis.

Jonathan ya yi wannan furuci ne bayan wasu magoya bayansa sun gudanar da tattaki zuwa gidansa suna rokon sa ya shiga takarar shugaban kasa.

2027: Zan yi shawara sosai – Jonathan ya nuna sha’awar takarar shugaban kasa

Da yake mayar da martani, Jonathan ya jaddada muhimmancin kishin kasa, zaman lafiya da gudanar da sahihin zabe a Najeriya.

“Takarar shugaban kasa ba wasan kwamfuta ba ne, amma na ji abin da kuka fada, kuma zan yi shawara sosai,” in ji Jonathan.

An kuma ga wani bidiyo da aka wallafa a ranar Juma’a wanda ke nuna yadda kotun ke shirin fara sauraron karar da ta shafi batun.

Siyasa
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

An shiga fargaba bayan barkewar Hantavirus a jirgin ruwa

May 8, 2026

“Wallahi Taallahi A Gaba Na Husaini Gimba Ya Kashe Dadiyata” – Muhammed Musa

May 8, 2026

2027: Zan yi shawara sosai – Jonathan ya nuna sha’awar takarar shugaban kasa

May 7, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • An shiga fargaba bayan barkewar Hantavirus a jirgin ruwa
  • “Wallahi Taallahi A Gaba Na Husaini Gimba Ya Kashe Dadiyata” – Muhammed Musa
  • Ana cikin fargaba yayin da kotu za ta fara sauraron karar cancantar Jonathan
  • 2027: Zan yi shawara sosai – Jonathan ya nuna sha’awar takarar shugaban kasa
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 7, Mayu. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.