’Yan Najeriya na cikin fargaba yayin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja za ta fara sauraron karar da ta shafi cancantar tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, wajen tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027.
Rahotanni sun bayyana cewa ana sa ran Jonathan zai bayyana a kotu da kansa a yau Juma’a domin ci gaba da shari’ar.
Wannan na zuwa ne kasa da awanni 24 bayan tsohon shugaban kasar ya nuna sha’awar tsayawa takara a zaben shugaban kasa mai zuwa yayin wani jawabi da ya yi a Abuja ranar Alhamis.
Jonathan ya yi wannan furuci ne bayan wasu magoya bayansa sun gudanar da tattaki zuwa gidansa suna rokon sa ya shiga takarar shugaban kasa.
2027: Zan yi shawara sosai – Jonathan ya nuna sha’awar takarar shugaban kasa
Da yake mayar da martani, Jonathan ya jaddada muhimmancin kishin kasa, zaman lafiya da gudanar da sahihin zabe a Najeriya.
“Takarar shugaban kasa ba wasan kwamfuta ba ne, amma na ji abin da kuka fada, kuma zan yi shawara sosai,” in ji Jonathan.
An kuma ga wani bidiyo da aka wallafa a ranar Juma’a wanda ke nuna yadda kotun ke shirin fara sauraron karar da ta shafi batun.
