Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Kotu Ta Dakatar da Rashida Mai Sa’a Daga Amfani da Social Media

Kotu Ta Dakatar da Rashida Mai Sa’a Daga Amfani da Social Media

By Ahmad Habib IbrahimMayu 11, 2026No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Kotun majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland a Kano, ƙarƙashin mai shariʼa Halima Wali ta hana jarumar Kannywood Rashida Adamu Mai Saʼa yin posting a social media har sai an gama shariʼar da Ruƙayya Dawayya ta yi ƙararta kan zargin ɓata suna.
Dawayya tana ƙarar Mai Saʼa ne bisa zargin ɓata mata suna da cin mutunci da hana zaman lafiya.
An zarge ta da cewa a ranar 15 ga Janairun 2026 ta yi wani bidiyo wanda ta yaɗa a kafafen sada zumunta, inda a ciki ta ci mutuncin Dawayya da cewai wai ta je wajen wani ɗan siyasa ta yi abin da bai dace ba a jihar Gombe.
Bayan karanta mata zargin ɓata suna, da cin mutunci da hana zaman lafiya duka ta musanta.
Lauyoyinta sun nemi a sanya ta a beli, inda kotun ta amince bisa sharaɗin za ta kawo ɗan majalisar jiha mai ci, da kuma ɗan uwanta wanda ya ke da gida ko fili da bai gaza Naira Miliyan 300 ba a Kano, Kotun ta kuma ayyana naira miliyan goma.
Sannan ta yi umarnin a karɓe wayoyinta, kuma kar ta kuma wallafa wani abu a shafukanta na kafafen sadarwa har sai an kammala shariʼar.
A karshe Kotun ta sanya ranar 20 ga watan Mayun da muke ciki domin ci gaba da shariʼar.

Arewa News Bata Suna Celebrity News Court Case Dawayya Hausa Celebrities Hausa Entertainment Hausa Film Jaruman Kannywood KANNYWOOD Kannywood News kano Kano Court Labaran Kannywood Mai Sa’a Rashida Mai Sa’a Ruqayya Dawayya Shari’a Social Media Ban Trending News
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN

Yuli 20, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026

Yuli 16, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026

Yuli 15, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026
  • Tsohon Ministan Kimiyya, Uche Nnaji ya musanta zargin ƙirƙirar takardun shaidar karatu
  • Gwamnatin Tarayya ta dakatar da ƙarin kuɗin jarabawar WAEC da NECO bayan suka
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.