Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Gwamnatin Borno: An Sake Shigar da Tsoffin ’Yan Boko Haram Sama da 8,000 Cikin Al’umma

Gwamnatin Borno: An Sake Shigar da Tsoffin ’Yan Boko Haram Sama da 8,000 Cikin Al’umma

By Ahmad Habib IbrahimMay 10, 2026No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Gwamnatin Jihar Borno ta bayyana cewa ta samu gagarumar nasara wajen sake dawo da tsoffin ’yan Boko Haram da iyalansu cikin al’umma, inda sama da mutane 8,000 aka riga aka sake haɗa su da rayuwar jama’a ta hanyar shirin gyaran hali da sake rayuwa.

Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta jihar, Zuwaira Gambo, ce ta bayyana hakan a Maiduguri yayin da take bayani kan nasarori da ƙalubalen shirin kawar da tsattsauran ra’ayi da sake haɗa tsoffin mayaƙan cikin al’umma.

Ta ce wannan shiri da gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum ke jagoranta, ya samu nasarar kusan kashi 75 cikin 100, kuma yana daga cikin manyan matakan dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

A cewarta, yawancin waɗanda suka miƙa wuya ba mayaƙa kai tsaye ba ne, illa mutane da ke bayar da tallafi da ayyukan baya ga ƙungiyar.

Ta bayyana cewa mafi yawan waɗanda aka karɓa mata da yara ne, waɗanda suka fito daga daji cikin matsanancin tashin hankali, matsalolin lafiya da rashin sanin rayuwar zamani.

“Waɗannan mata sun fito ne da raunukan zuciya, cin zarafin jinsi da matsalolin tunani,” in ji ta.

Kwamishiniyar ta ƙara da cewa wasu daga cikin yaran ba su taɓa rayuwa a cikin tsari na gari ko ganin kayayyakin more rayuwa na zamani ba kafin zuwansu cibiyoyin gyaran hali.

Gwamnatin jihar ta ce ta samar da jami’an jin ƙai, makarantu na wucin gadi, cibiyoyin lafiya da shirye-shiryen koyon sana’o’i domin taimaka wa waɗanda aka sake tsugunarwa.

Haka kuma, ta musanta zargin cewa wasu daga cikin waɗanda aka gyara suna komawa cikin ayyukan ta’addanci, tana mai cewa galibin ƙungiyoyin da suka bari suna ƙin karɓarsu idan suka miƙa wuya.

Arewa Maso Gabas Boko haram BORNO Gyaran Hali Hausa News Maiduguri Najeriya Najeriya Today tsaro Zulum
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 11, Mayu. 2026

May 11, 2026

An shiga fargaba bayan barkewar Hantavirus a jirgin ruwa

May 8, 2026

“Wallahi Taallahi A Gaba Na Husaini Gimba Ya Kashe Dadiyata” – Muhammed Musa

May 8, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 11, Mayu. 2026
  • Gwamnatin Borno: An Sake Shigar da Tsoffin ’Yan Boko Haram Sama da 8,000 Cikin Al’umma
  • An shiga fargaba bayan barkewar Hantavirus a jirgin ruwa
  • “Wallahi Taallahi A Gaba Na Husaini Gimba Ya Kashe Dadiyata” – Muhammed Musa
  • Ana cikin fargaba yayin da kotu za ta fara sauraron karar cancantar Jonathan
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.