Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026

By Ahmad Habib IbrahimYuli 15, 2026No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email
Demo

1. An kama Adeniyi Adeyemi, Darakta Janar na kungiyar PFIPC, bayan kotu ta ba da umarnin cafke shi saboda rashin halartar shari’arsa.

2. Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bukaci Majalisar Wakilai ta gyara Kundin Tsarin Mulki domin ba wa jihohi damar kafa ‘yan sandan jiha (State Police) don inganta tsaro.

Demo

3. Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa Muhammad Sani hukuncin daurin shekaru 20, bayan samunsa da laifin boye bayanan wani fitaccen dan bindiga mai suna Danranmi.

4. Rundunar ‘yan sandan Legas ta bankado wata kungiyar damfara da ake zargi da satar motocin alfarma ta hanyar yaudara, inda aka ce sun damfari dillalan motoci fiye da Naira biliyan 1.

5. ‘Yan sanda na ci gaba da neman wadanda suka harbe suka kashe Toba Ajiboye (Toba Ijaya), Sakataren Shirye-shirye na kungiyar NURTW a Legas.

6. Bayan kwanaki 56 a hannun masu garkuwa, dalibai da malamai da aka ceto daga garkuwa a Oriire, jihar Oyo, sun koma hannun iyalansu cikin farin ciki da hawaye.

7. Wata kotun bincike a Birtaniya ta tabbatar da cewa Beatrice Solomon, ‘yar Najeriya mai shekara 27, ta mutu ne ta hanyar kashe kanta bayan fama da matsalolin lafiyar kwakwalwa.

8. Ana zargin makiyaya dauke da makamai sun sake kai hari a wata al’umma da ke karamar hukumar Otukpo, jihar Benue, inda suka kashe mutum guda.

9. Rundunar ‘yan sanda ta jihar Rivers ta kama wani mutum mai suna Richard, bisa zargin kashe budurwarsa Caroline Sunday bayan rikicin da ya shafi zargin cin amana.

10. Tsohon Mataimakin Shugaban PDP na kasa, Chief Olabode George, ya yi gargadin cewa ana kokarin amfani da kotuna da hukumomin gwamnati wajen tayar da rikici da raunana jam’iyyar PDP kafin zaben 2027.

Demo
Labaran Safiyar Yau
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN

Agusta 26, 2026

Nijar ta cimma yarjejeniyar gina tashar hasken rana mai karfin megawatt 200

Agusta 26, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 26, Agusta. 2026

Agusta 26, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN
  • Nijar ta cimma yarjejeniyar gina tashar hasken rana mai karfin megawatt 200
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 26, Agusta. 2026
  • Me Ya Sa Mutum Lake Aiki Tukuru Amma Har Yanzu Yake Cikin Talauci?
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 18, Agusta. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.