Tsohon Ministan Ƙirƙire-ƙirƙire, Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji, ya musanta zargin da ake masa na ƙirƙirar takardar shaidar digirinsa da kuma takardar kammala aikin bautar ƙasa (NYSC) bayan gwamnatin tarayya ta gurfanar da shi a kotu.
Hukumar ICPC (Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission) ce ta shigar da ƙarar, kuma an gurfanar da shi a gaban Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.
Ana tuhumar Nnaji da laifuffuka guda shida, ciki har da zargin ƙirƙirar takardar digiri daga Jami’ar Najeriya da ke Nsukka (UNN) da kuma takardar kammala bautar ƙasa ta NYSC, waɗanda ya gabatar yayin tantance shi a matsayin minista a shekarar 2023.
Har ila yau, ana zarginsa da karɓar kusan Naira miliyan 29.5 a matsayin albashi da wasu alawus-alawus ta hanyar yaudara, tare da zargin safarar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba.
Bayan ya musanta dukkan tuhume-tuhumen a ranar Litinin, lauyan gwamnati ya sanar da kotu cewa ya shirya fara shari’ar, inda ya bayyana cewa shaidu uku sun riga sun hallara a kotun.
Sai dai lauyan Nnaji, Ogwu Onoja (SAN), ya nemi ƙarin lokaci domin shirya kare wanda yake wakilta, tare da sanar da kotu cewa sun riga sun shigar da buƙatar beli tun ranar 9 ga Yuli.
Lauyan gwamnati bai yi adawa da neman belin ba.
A hukuncin da ta yanke, Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta ba Nnaji beli kan kuɗin Naira miliyan 20, tare da sharadin gabatar da mutum ɗaya da zai tsaya masa, wanda dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai matsayi ba ƙasa da Level 15, kuma mazaunin Abuja.
Kotun ta kuma umarce shi da ya miƙa fasfo ɗinsa na aiki da na kansa har zuwa lokacin da za a kammala shari’ar.
Rahotanni sun ce gurfanar da Nnaji ya biyo bayan watanni na bincike kan sahihancin takardunsa, inda aka ruwaito cewa Jami’ar UNN da Hukumar NYSC sun musanta sahihancin takardun da ake magana a kansu.
An kama Nnaji ne a ranar 30 ga Yuni, 2026, a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, lokacin da jami’an DSS suka tsare shi bayan ya dawo daga Enugu.
An ce an kama shi ne bisa umarnin kotu da aka bayar tun ranar 11 ga Yuni, 2026, bayan ya kasa amsa gayyata da dama domin amsa tambayoyi a binciken da ake yi.
Nnaji ya yi murabus daga mukaminsa na minista a ranar 7 ga Oktoba, 2025, inda ya bayyana cewa ya yi hakan ne domin mutunta tsarin shari’a, yayin da ya ci gaba da musanta aikata wani laifi, yana mai cewa akwai siyasa a bayan shari’ar.
A halin yanzu, Uche Nnaji shi ne ɗan takarar gwamnan jihar Enugu na jam’iyyar PDP.
