Takaitattun Labaran Najeriya na Yau
1. Majalisar Wakilai za ta kada kuri’a kan kafa ‘yan sandan jihohi
Majalisar Wakilai ta bayyana cewa za ta yi kuri’a kan gyaran kundin tsarin mulki domin bai wa jihohi da ƙananan hukumomi damar kafa nasu rundunar ‘yan sanda, a matsayin wata hanya ta magance matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara a ƙasar.
2. Gobara ta tayar da hankula a Majalisar Dattawa
Wata gobara da ta tashi daga wani sashe na girki a ginin Majalisar Dattawa da ke Abuja ta haddasa firgici, inda sanatoci, ma’aikata da baƙi suka yi gaggawar ficewa kafin aka shawo kan lamarin.
3. Majalisar Dattawa ta bayar da umarnin kama Mele Kyari
Kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da Asusun Jama’a ya bayar da umarnin kama tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kyari, bisa zargin kin amsa gayyatar da aka yi masa domin bayyana a gaban kwamitin.
4. ‘Yan sanda sun kashe ‘yan bindiga biyu a Abuja
Rundunar ‘Yan Sandan Babban Birnin Tarayya ta sanar da kashe wasu ‘yan bindiga biyu da ake zargi suna addabar mazauna Abuja a wani samame da kwamishinan ‘yan sandan FCT ya jagoranta.
5. Mahara sun kashe mutum uku a Kogi
Mazauna ƙauyen Iluke da ke Jihar Kogi sun nemi agajin gwamnati bayan wani hari da wasu mahara suka kai ya yi sanadin mutuwar mutum uku, ciki har da mataimakin shugaban makaranta.
6. Gwamnati ta ba da umarnin binciken jirgin sama da ya sauka a hanya
Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya ba da umarnin bincike kan yadda wani jirgin sama ya sauka tare da tashi daga wata hanya a yankin Ogwashi-Uku da ke Jihar Delta.
7. Gwamnan Adamawa ya umarci masu riƙe da muƙamai su yi murabus idan sun sauya jam’iyya
Gwamna Ahmadu Fintiri ya umarci duk masu riƙe da muƙaman siyasa a gwamnatinsa da suka koma wata jam’iyya daban su yi murabus nan take ko kuma a kore su.
8. Sojoji da DSS sun gano ma’ajiyar makamai a Enugu
Sojoji tare da jami’an DSS sun ce sun gano wata ma’ajiyar makamai da ake zargin tana da alaƙa da ƙungiyar IPOB da reshen ta na ESN a Jihar Enugu.
9. Tsofaffin ma’aikatan Arab Bank da Assurance Bank sun yi zanga-zanga
Wasu tsofaffin ma’aikatan bankunan Arab Bank da Assurance Bank sun gudanar da zanga-zanga a Legas, suna zargin hukumomi da yin watsi da su tare da jefa su cikin matsanancin talauci.
10. Ɗalibai sun tsere daga makarantu a Minna saboda fargabar harin ‘yan bindiga
Dalibai a babban birnin Jihar Neja, Minna, sun watse daga makarantu kafin lokacin tashi saboda jita-jitar cewa ‘yan bindiga sun shiga yankin.
