Author: Ahmad Habib Ibrahim

Kamfanin mai na Dangote ya rage farashin man fetur (PMS) a fadin ƙasar, tare da sanar da 15 ga Satumba, 2025 a matsayin sabon ranar da zai fara rabawa kai tsaye ga masu amfani. Shirin, wanda aka shirya a fara tun 15 ga Agusta, zai bai wa matatar mai ta dala biliyan $20 damar rarraba fetur da dizal kai tsaye ga jama’a ta hanyar motoci 4,000 na iskar gas (CNG) ba tare da kuɗin jigilar kaya ba. Matatar mai wacce ke da ƙarfin tace ganga 650,000 a rana ta ce farashin man gantry ya kasance N820 kowace lita, kamar yadda aka sanar da shi a watan da…

Read More

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta samu Mahmud Usman, ɗaya daga cikin kwamandojin ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru, da laifi tare da ɗaurin shekara 15 a gidan yari. Usman, wanda aka fi sani da Abu Barra, hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta gurfanar da shi a gaban kotu, inda ya amsa laifin haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba. Takardar tuhumar ta nuna cewa wannan laifi ya ba shi damar sayen makamai domin gudanar da ta’addanci da garkuwa da mutane. Alƙalin kotun, Maishari’a Emeka Nwite, ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare shi a hannun DSS har zuwa lokacin da za…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 12 Ga Satumba, 2025 📰 1. FG ta soke harajin kashi 5% kan kiran waya da intanet Gwamnatin tarayya ta soke harajin kashi 5% da aka saka kan ayyukan kiran waya da intanet. Hukumar Wayar Da Kai ta Ƙasa (NOA) ce ta sanar da sokewar harajin a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis. 📰 2. IGP Egbetokun ya ce ’yan ta’adda sun fi jami’an tsaro wayewa Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa, Kayode Egbetokun, ya amince cewa masu laifi da ke addabar ’yan Najeriya a sassa daban-daban na ƙasar sun sha gaban jami’an tsaro ta…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 10 Ga Satumba, 2025 📰 1. DSS ta sasanta rikici tsakanin Dangote Group da NUPENG Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta sasanta rikicin da ke tsakanin Kamfanin Dangote da Ƙungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Gas (NUPENG) kan batun kafa ƙungiya. Bayan wani taro da aka gudanar a bayan ƙofa a babban ofishin DSS da ke Abuja, an bayyana cewa shugabancin NUPENG ya umurci mambobinta da su dakatar da yajin aikin kasa baki ɗaya. 📰 2. Shugaban APC ya ce ƙarin gwamnoni za su shiga jam’iyyar kafin 2027 Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 9 Ga Satumba, 2025 📰 1. TUC ta yi watsi da harajin mai kashi 5% da gwamnati ta shirya Kungiyar Kwadago ta TUC a ranar Litinin ta yi watsi da shirin gwamnatin tarayya na sanya harajin kashi 5% kan kayayyakin mai, tana mai cewa wannan “mummunar dabi’ar tattalin arziki ce.” TUC ta bukaci gwamnati ta janye shirin cikin kwanaki 14, inda ta yi barazanar dakatar da muhimman sassa na kasar idan ba a yi hakan ba. 📰 2. El-Rufai ya kai ƙara ga PSC da IGP kan laifukan ’yan sanda a Kaduna Tsohon Gwamnan Kaduna,…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 8 Ga Satumba, 2025 1. Ministan Kwadago ya kira taron gaggawa tsakanin Dangote da NUPENG Ministan Kwadago da Ayyuka, Muhammadu Dingyadi, ya kira shugabancin kamfanin Dangote Group da kuma kungiyar NUPENG zuwa taron gaggawa a yau, domin dakatar da shirin yajin aikin ƙasa baki ɗaya. Ana zargin kamfanin da manufofin da ba sa goyon bayan ‘yan ƙungiya. 2. ADC ta zargi APC da yin kama da ƙungiyar ta’addanci a Lagos Jam’iyyar ADC ta zargi jam’iyyar APC mai mulki da yin kama da ƙungiyar ta’addanci, bayan wani hari da aka kai wa mambobinta a filin coci…

Read More

Gwamnatin Tarayya karkashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu ta ayyana ranar Juma’a, 5 ga Satumba, 2025, a matsayin hutun gwamnati domin bikin tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW). A wata sanarwa da Sakataran Dindindin na Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Dr Magdalene Ajani ta fitar a ranar Talata, Ministan Harkokin Cikin Gida, Dr Olubunmi Tunji-Ojo, ya yi wannan sanarwa a madadin gwamnatin tarayya. Ministan ya mika gaisuwar fatan alheri ga musulmai a Najeriya da ma duniya baki ɗaya, yana mai kira ga al’ummar Musulmi da su yi koyi da dabi’un Annabi Muhammad (SAW) na zaman lafiya, soyayya, tawali’u, hakuri da tausayawa. Ya ce waɗannan halaye…

Read More