Author: Ahmad Habib Ibrahim

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana damuwa cewa alkalan Najeriya sun lalace ƙwarai sakamakon cin hanci da rashawa, wanda ya mayar da kotunan ƙasar “kotun rashawa” maimakon “kotun adalci”. A sabon littafinsa mai suna “Nigeria: Past and Future”, Obasanjo ya yi bayani cewa: Obasanjo ya gargadi cewa idan adalci zai ci gaba da zama abin siye, to ƙasa za ta fuskanci tashin hankali, fitina da anarchy maimakon kwanciyar hankali da ci gaba.

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 22 Ga Agusta, 2025 1. Rikicin Zoning PDP:Wasu shugabannin PDP na jihohi daga Kudancin Najeriya, da wasu ‘yan majalisa da tsoffin mambobin NWC sun nesanta kansu daga taron Zoning da ake yi a Legas. Taron na Legas zai yanke hukunci kan matsayar Kudancin PDP wajen rabon mukamai. 2. Harin Plateau:Aƙalla manoma 15 aka kashe a sabuwar hari a ƙauyuka bakwai na Chakfem LGA, Mangu, Plateau. Masu harin sun ƙone gidaje da sace dabbobi. 3. Harin Kaduna:‘Yan bindiga sun kai hari Kakangi, Birnin Gwari (Kaduna), inda suka kashe manoma 5 – 4 daga cikin su dangi…

Read More

Tel Aviv, Isra’ila —Rahotanni sun bayyana cewa Isra’ila na tattaunawa da Kudancin Sudan kan yiwuwar karɓar Falasdinawa daga zirin Gaza domin sake tsugunar da su a ƙasar, wanda har yanzu ke fama da yaƙi da talauci. Mutane shida da suka san da lamarin sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na AP cewa an fara tattaunawa, duk da cewa ba a fayyace matakin da aka kai ba. Idan aka aiwatar, wannan shirin zai iya zama kamar mayar da jama’a daga wuri mai fama da yaƙi da yunwa zuwa wani wuri mai irin wannan matsala, lamarin da ya jawo ƙarar naƙasu daga kungiyoyin kare…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 20 Ga Agusta, 2025 1. Harin Katsina – Akalla mutum 13 suka mutu, da dama kuma sun jikkata a harin da aka kai wa al’ummar Unguwar Mantau, Malumfashi, Katsina, a lokacin da suke sallar Asuba. 2. Tsaro a jirgin sama – Hukumar NCAA ta umarci cewa dukkan wayoyi da na’urorin lantarki a kashe su yayin matakan da suka fi muhimmanci a tafiyar jirgin. 3. Shari’ar harin Owo – DSS ta roki kotun tarayya da ke Abuja kada ta ba da belin mutum biyar da ake tuhuma da harin Cocin Katolika na Owo a 2022, saboda alaƙarsu da ƙungiyoyin ta’addanci na ƙasashen…

Read More

A yau aka shirya taron musamman a Fadar White House tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky, tare da manyan shugabannin Turai da wakilan EU da NATO. Taron ya zo ne domin tattauna yadda za a kawo karshen yakin da ya shafe shekaru uku tsakanin Ukraine da Rasha. Abin da kowanne bangare ke nema: 🔹 Trump/Amurka: 🔹 Ukraine/Zelensky: 🔹 Turai (UK, Jamus, Faransa, Italiya, Finland, EU, NATO): 🔹 Rasha (Putin): ✍️ Kammalawa:Taron na yau zai iya zamewa muhimmin mataki a makomar Ukraine da tsaron Turai. Kowanne bangare na neman abinda zai amfanar da shi, amma babban kalubale shine yadda za a cimma matsaya ba tare…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 18 ga Agusta, 2025 1. Akalla ’yan kasuwa 30, ciki har da mata, ake zargin sun rasu a wani hatsarin kwale-kwale da ya auku a ranar Lahadi a kauyen Kojiyo, karamar hukumar Goronyo, jihar Sokoto. Rahotanni sun bayyana cewa mutanen na kan hanyarsu ta zuwa kasuwar mako-mako ta Goronyo ne lokacin da kwale-kwalen da ke ɗauke da fasinjoji da kaya ya kife misalin ƙarfe 1:30 na rana. 2. Sarkin Zuru na jihar Kebbi, Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya), wanda aka fi sani da Gomo II, ya rasu yana da shekara 81. Marigayin ya rasu a asibiti…

Read More