Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Eid-ul-Mawlid: Gwamnatin Tinubu ta ayyana hutun ranar Juma’a

Eid-ul-Mawlid: Gwamnatin Tinubu ta ayyana hutun ranar Juma’a

By Ahmad Habib IbrahimSatumba 3, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email
Demo

Gwamnatin Tarayya karkashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu ta ayyana ranar Juma’a, 5 ga Satumba, 2025, a matsayin hutun gwamnati domin bikin tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

A wata sanarwa da Sakataran Dindindin na Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Dr Magdalene Ajani ta fitar a ranar Talata, Ministan Harkokin Cikin Gida, Dr Olubunmi Tunji-Ojo, ya yi wannan sanarwa a madadin gwamnatin tarayya.

Demo

Ministan ya mika gaisuwar fatan alheri ga musulmai a Najeriya da ma duniya baki ɗaya, yana mai kira ga al’ummar Musulmi da su yi koyi da dabi’un Annabi Muhammad (SAW) na zaman lafiya, soyayya, tawali’u, hakuri da tausayawa. Ya ce waɗannan halaye na da matuƙar muhimmanci wajen gina ƙasa mai haɗin kai da cigaba.

Haka kuma, ya yi kira ga ‘yan Najeriya na dukkan addinai da su yi amfani da wannan lokaci wajen yi wa ƙasa addu’a domin zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali, tare da goyon bayan ƙoƙarin gwamnati na samar da daidaito da ci gaban dorewa.

“Bikin Eid-ul-Mawlid yana bamu wata dama ta ƙarfafa zumunci, inganta zaman lafiya a tsakanin al’umma, da kuma koyon darussan Annabi na mutunta juna da sadaukar da kai don jin ƙai,” in ji Tunji-Ojo.

Ya ƙara da jan hankalin ‘yan ƙasa da su kasance masu bin doka, masu lura da tsaro, tare da tallafa wa manufofin gwamnati da nufin inganta walwalar kowa. Ya kuma yi fatan Musulmi za su yi biki cikin farin ciki da kwanciyar hankali.

Demo
Maulud Mouloud
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Sarkin Gumel Alhaji Dr. Ahmed Muhammad Sani II, CON Ya Rasu A Yau 3 Ga Nuwamba 2026

Satumba 3, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 2, Nuwamba 2026

Satumba 2, 2026

Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN

Agusta 26, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Sarkin Gumel Alhaji Dr. Ahmed Muhammad Sani II, CON Ya Rasu A Yau 3 Ga Nuwamba 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 2, Nuwamba 2026
  • Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN
  • Nijar ta cimma yarjejeniyar gina tashar hasken rana mai karfin megawatt 200
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 26, Agusta. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.