Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Kamfanin Mai na Dangote ya rage farashin man fetur

Kamfanin Mai na Dangote ya rage farashin man fetur

By Ahmad Habib IbrahimSatumba 12, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email
Demo

Kamfanin mai na Dangote ya rage farashin man fetur (PMS) a fadin ƙasar, tare da sanar da 15 ga Satumba, 2025 a matsayin sabon ranar da zai fara rabawa kai tsaye ga masu amfani.

Shirin, wanda aka shirya a fara tun 15 ga Agusta, zai bai wa matatar mai ta dala biliyan $20 damar rarraba fetur da dizal kai tsaye ga jama’a ta hanyar motoci 4,000 na iskar gas (CNG) ba tare da kuɗin jigilar kaya ba.

Demo

Matatar mai wacce ke da ƙarfin tace ganga 650,000 a rana ta ce farashin man gantry ya kasance N820 kowace lita, kamar yadda aka sanar da shi a watan da ya gabata.

A sabon tsarin farashin da kamfanin ya fitar a shafinsa na X, an bayyana cewa a Lagos, Oyo, Ogun, Ondo da Ekiti, farashin man fetur zai kasance N841 kowace lita, daga N860.

A Abuja, Edo, Delta, Rivers da Kwara, farashin zai kasance N851 kowace lita, wanda ya ragu daga N885. Wannan na nufin akwai ragi na N19 a jihohin Kudu maso Yamma, da kuma ragi na N34 a Abuja, Arewa ta Tsakiya da yankin Kudu maso Kudu.

Sabon tsarin farashin da shirin rabawa kai tsaye zai fara aiki daga Litinin, 15 ga Satumba, 2025.

Sai dai, rahoton DAILY POST ya bayyana cewa sabon tsarin farashin na Dangote ba ya daure sauran ’yan kasuwa da masu sayar da mai, banda MRS da sauran abokan rabon su kai tsaye.

Wannan na zuwa ne yayin da ƙungiyar NUPENG ta yi barazanar komawa yajin aiki, tana zargin Dangote da karya yarjejeniyar da aka cimma kwanan nan. A martaninsa, Dangote ya bayyana cewa yana mutunta ’yancin ma’aikata na shiga ƙungiyoyin kwadago idan suna so.

Demo
Dangote labarai
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Sarkin Gumel Alhaji Dr. Ahmed Muhammad Sani II, CON Ya Rasu A Yau 3 Ga Nuwamba 2026

Satumba 3, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 2, Nuwamba 2026

Satumba 2, 2026

Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN

Agusta 26, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Sarkin Gumel Alhaji Dr. Ahmed Muhammad Sani II, CON Ya Rasu A Yau 3 Ga Nuwamba 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 2, Nuwamba 2026
  • Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN
  • Nijar ta cimma yarjejeniyar gina tashar hasken rana mai karfin megawatt 200
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 26, Agusta. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.