Wani Kanal na Sojin Najeriya, Mohammed Ma’aji, ya bayyana babban dalilin da ya sa shi da wasu jami’an soji suka shirya juyin mulki domin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
A cewar Premium Times, Ma’aji ya ce matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara, cin hanci da rashawa da kuma tsananin matsin tattalin arziki na daga cikin manyan ƙorafe-ƙorafen da waɗanda ake zargin suna da hannu a shirin juyin mulkin suka tattauna.
Ma’aji ya ce tattaunawar neman sa hannun soji a harkokin mulkin ƙasa ta fara ne tun shekarar 2023, a ƙarshen mulkin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari.
Ya ce:
“Abubuwa sun fara fita daga iko musamman a ƙarshen mulkin Buhari, lokacin da cin hanci da rashawa da son kai suka zama ruwan dare.”
Kanal Ma’aji ya bayyana cewa yana ganin manyan jami’an soji ya kamata su ɗauki mataki mai ƙarfi domin magance matsalar tsaron da ke ƙara tabarbarewa. Daga nan ne, a cewarsa, ƙungiyar ta fara gano wasu jami’an soji da suke da irin wannan ra’ayi.
Ya ce yawancin jami’an da ake zargin suna da hannu a shirin suna da kishin ƙasa, son Najeriya da kuma burin ganin an samu sauyi mai kyau.
Ma’aji ya kuma bayyana cewa an dakatar da shirin tun farko saboda rashin isassun kuɗaɗe, kayan aiki da ma’aikata. Ya yi ikirarin cewa mafi yawan kuɗin da aka fara amfani da su sun fito ne daga aljihunsa.
Ya ce wani Manjo a cikin sojojin ya bayar da Naira miliyan ɗaya, yayin da wani jami’i kuma ya bayar da dala a lokuta daban-daban.
Jami’in sojan ya bayyana cewa an sake farfaɗo da shirin bayan da a karo na biyu ya kasa samun ɗaukaka zuwa matsayin Brigadier General a shekarar 2024. Sai dai ya jaddada cewa rashin samun ɗaukakar ba shi ne babban dalilin shirin ba.
Daga cikin abubuwan da Ma’aji ya ce suka jawo rashin gamsuwa sun haɗa da:
- Cire tallafin man fetur.
- Sauye-sauyen tsarin musayar kuɗi.
- Sabbin manufofin haraji.
- Ƙarin kuɗin wutar lantarki.
- Cin hanci da rashawa.
- Tabarbarewar tsaro.
- Matsalar rashin aikin yi da tsananin wahalar rayuwa.
Ya kuma ambaci yadda aka tunkari zanga-zangar #EndSARS da #EndBadGovernance, yana mai cewa matasa da dama sun shiga cikin takaici saboda rashin aikin yi da matsin tattalin arziki.
