Author: Ahmad Habib Ibrahim

Labaran Najeriya Na Yau – 4 Ga Nov, 2025 1. Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 19 A Kano:Akalla ’yan bindiga 19 aka kashe yayin arangama da dakarun Operation MESA a karamar hukumar Shanono, Jihar Kano. Sojoji biyu da ɗan banga ɗaya sun rasu a yayin fafatawar da ta faru daren Asabar karkashin 3 Brigade ta rundunar sojin Najeriya. 2. ’Yan Sanda A Lagos Sun Bayyana Omoyele Sowore A Matsayin Wanda Ake Nema:Rundunar ’yan sandan Jihar Lagos ta bayyana ɗan gwagwarmaya kuma ɗan siyasa Omoyele Sowore a matsayin wanda ake nema saboda zargin shirin tayar da tarzoma da toshe manyan hanyoyi. Kwamishinan ’yan sanda Olohundare Jimohne ya bayyana…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 31 Ga Oct, 2025 1. Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Nadin Dr. Bernard Doro A Matsayin Minista:Majalisar Dattawa ta amince da nadin Dr. Bernard Doro a matsayin sabon minista bayan tantancewa da ta ɗauki kasa da minti 30. Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya halarci zaman majalisar yayin tabbatarwar. 2. Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Hafsoshin Tsaro Sabon Kambun Mukami:Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanya wa sabbin hafsoshin tsaro kambun mukamansu a fadar shugaban ƙasa, Abuja. A ciki akwai Janar Olufemi Oluyede a matsayin shugaban rundunar tsaro (CDS) da Lieutenant Janar Emmanuel Undiendeye a matsayin shugaban leken asiri na soji…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 29 Ga Oct, 2025 1. Gwamnatin Amurka ta soke takardar izinin shiga ƙasar (visa) ta B1/B2 da aka bai wa fitaccen marubuci kuma mai lambar yabo ta Nobel, Farfesa Wole Soyinka. Soyinka ya bayyana hakan yayin taron manema labarai mai taken “Unending Saga: Idi Amin in Whiteface!” a Freedom Park, Lagos, ranar Talata. 2. Majalisar Dattawa za ta fara tantance sabbin manyan hafsoshin tsaro da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya mika sunayensu gobe Laraba. Tinubu ya aika da wasikar neman tabbatar da su zuwa majalisar. 3. Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta gargadi jami’an tsaro da aka tura don zaɓen…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 28 Ga Oct, 2025 1. Shugaba Tinubu Ya Sadu Da Sabbin Hafsoshin Tsaro: Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da sabbin hafsoshin tsaro a fadar gwamnati, Abuja, a ranar Litinin. Wannan ganawa ce ta farko tun bayan nada su kwanaki uku da suka gabata, kuma an gudanar da ita a bayan ƙofa. 2. Nnamdi Kanu Ya Fasa Kiran Shaidu A Kotu: Shugaban haramtacciyar kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, ya sanar wa kotu cewa ya janye shirin kiran shaidu domin kare kansa, yana mai cewa babu wani hujja da ke tabbatar da laifin da ake tuhumar…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 24 Ga Oct, 2025 1. Sabon Shugaban INEC Ya Kama Aiki: Sabon shugaban hukumar zabe ta kasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, ya kama aiki a yau Alhamis bayan rantsuwar da Shugaba Bola Tinubu ya yi masa a fadar shugaban kasa. Ya ce ba za a taɓa yin wasa da sahihancin tsarin zaben Najeriya ba. 2. PDP Za Ta Fara Tantance ’Yan Takararta: Jam’iyyar PDP ta sanar da cewa za ta fara tantance ’yan takara da ke neman mukamai daban-daban a babban taron jam’iyyar da ke tafe a ranar Talata, 28 ga Oktoba, a Legacy House,…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 23 Ga Oct, 2025 1. Shari’ar Nnamdi Kanu: Shugaban haramtacciyar kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, ya kammala tattaunawar sirri da tawagar lauyoyinsa karkashin jagorancin tsohon Babban Lauyan Tarayya, Kanu Agabi. Ana sa ran fara kare kansa a kotu ranar Alhamis, 23 ga Oktoba. 2. Zaben Shugaban Jam’iyyar PDP: Shugabannin PDP daga Arewa, ciki har da gwamnoni, sun amince da tsohon Ministan Harkokin Musamman, Tanimu Turaki, a matsayin dan takarar hadin kai don kujerar shugaban jam’iyyar a babban taron da za a gudanar a watan Nuwamba. 3. Akpabio Ya Yaba Da Zabukan Najeriya: Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 22 Ga Oct, 2025 1. An ƙona sakatariyar jam’iyyar ADC a Ado-Ekiti Wasu da ake zargin ’yan daba ne suka ƙona sakatariyar jam’iyyar ADC da ke yankin Basiri, Ado-Ekiti a daren Litinin. Wuta ta lalata kujeru, kayan ofis, lasifika da sauran kayan aiki. 2. Kotu ta soke zaɓen kananan hukumomi a Ebonyi Babbar kotun tarayya da ke Abakaliki ta soke zaɓen kananan hukumomi da aka gudanar a watan Yuli 2024 a Jihar Ebonyi. Mai shari’a Hillary Oshomah ya ce zaɓen bai bi tanadin dokar zaɓe ba. 3. Gobarar mota mai ɗauke da fetur ta kashe mutane a Neja Mutane…

Read More