Author: Ahmad Habib Ibrahim

Labaran Najeriya Na Yau – 18 Ga Dec, 2025 1. Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da sakin wani jirgin saman Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) tare da jami’ansa 11 da aka tsare a ƙasar Burkina Faso bayan saukar gaggawa da suka yi. Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje, Kimiebi Ebienfa, ya sanar da hakan a daren Laraba, inda ya ce a taƙaice: “Eh, an sake su.” 2. Sabon gwamnan Jihar Rivers da ya sauya sheƙa, Siminalayi Fubara, ya kai ziyara ba tare da an sanar ba zuwa hedkwatar jam’iyyar APC ta ƙasa a daren Laraba. Fubara ya isa sakatariyar jam’iyyar da misalin…

Read More

Sabon rikicin da ya sake ɓarkewa tsakanin Alhaji Aliko Dangote, Shugaban Kamfanin Dangote Refinery, da Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Mai na Midstream da Downstream ta Ƙasa (NMDPRA), Farouk Ahmed, tare da masu shigo da man fetur da ‘yan kasuwa, ya jawo saukar farashin man fetur zuwa mafi ƙanƙanta a faɗin ƙasar. A ranar Lahadi, Dangote ya yi jerin zarge-zarge kan shugaban NMDPRA, ciki har da kiran sa “mai lalata tattalin arziki”, bisa dalilin ƙarfafa shigo da man fetur duk da cewa matatar Dangote na da isasshen ƙarfin tacewa. Attajirin ya kuma yi zargin cewa Farouk Ahmed ya kashe har…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 13 Ga Nov, 2025 1. Majalisar Dattawa ta amince da rancen cikin gida na N1.15 tiriliyan Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaba Bola Tinubu na ɗaukar rancen cikin gida na N1.15 tiriliyan domin cike gibin kasafin kuɗin shekara ta 2025. Wannan ya biyo bayan rahoton da kwamitin Majalisar kan Basussuka na cikin gida da na waje ya gabatar. 2. Gwamnati ta soke tsarin koyarwa da harshen gida Gwamnatin Tarayya ta soke manufar amfani da harsunan gida wajen koyarwa a makarantu. Ta ce tsarin ya haifar da mummunan sakamako a jarrabawar jama’a, inda dalibai ke…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 11 Ga Nov, 2025 1. Obasanjo ya ce Jimmy Carter ba ya yin komai a Afirka ba tare da saninsa ba Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa a lokacin da yake jagorancin Najeriya, marigayi shugaban Amurka Jimmy Carter ba ya ɗaukar mataki a Afirka ba tare da tuntubarsa ba. Wannan kalami ya zama abin fahimta kai tsaye kan cece-kuce da ke tattare da barazanar Donald Trump game da mamayar soja a ƙasar. 2. Timi Sylva zai mika kansa ga EFCC Mai magana da yawun tsohon Gwamnan Jihar Bayelsa, Julius Bokoru, ya ce Timipre…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 10 Ga Nov, 2025 1. Burtaniya ta gargadi ’yan ƙasarta kan tafiya Najeriya Ma’aikatar Harkokin Waje ta Birtaniya (FCDO) ta gargadi ’yan ƙasarta da su guji tafiya jihohi 21 a Najeriya saboda yawaitar rashin tsaro, garkuwa da mutane, da rikice-rikicen ƙabilanci. Hukumar ta ce wannan gargadin ya sabunta ne ranar Lahadi, 9 ga Nuwamba, 2025. 2. INEC ta bayyana Soludo a matsayin wanda ya lashe zaben Anambra Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) ta bayyana Gwamna Charles Soludo na jam’iyyar APGA a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Anambra. Ya doke ’yan takarar APC, PDP,…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau –6 Ga Nov, 2025 Majalisar Dattawa ta nuna damuwa kan asarar man fetur da ake zargin Najeriya ta yi fiye da dala biliyan $300saboda sata da rashin tsari a yankin Neja-Delta. Rahoton wucin gadi na kwamiti ƙarƙashin Sanata Ned Nwoko ya bayyana hakan. Bangaren PDP na Nyesom Wike ya soke taron gangamin jam’iyyar na kasa, bisa hujjar cewa ci gaba da shiryawa zai sabawa hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. Shugaban Sojin Sama, Air Marshal Sunday Aneke, ya kira dukkan kwamandojin rundunar sojin sama don ba su sabbin umarni kan yaƙi da ta’addanci a fadin ƙasar. Majalisar Dattawa ta dakatar da tabbatar…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 5 Ga Nov, 2025 Sojojin Najeriya sun ce sun hana ’yan ta’adda kai hari kan sansanin Forward Operating Base (FOB) Kangar da ke Mallam Fatori, Jihar Borno. Rundunar ta tabbatar da cewa an kashe da dama daga cikin mayakan Boko Haram da ISWAP a fafatawar da ta faru da safiyar Talata. Kotu a Ibadan ta bai wa jam’iyyar PDP damar ci gaba da taron gangamin ta na kasa da aka tsara don Nuwamba 15 zuwa 16, 2025 a Ibadan, bayan ta amince da bukatar da aka gabatar a gaban mai shari’a Ladiran Akintola. Kotu a Abuja ta umurci jagoran IPOB, Nnamdi Kanu, da ya kare kansa…

Read More