Author: Ahmad Habib Ibrahim

Labaran Najeriya Na Yau – 23 Ga Afrilu, 2026 1. Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya ajiye mukaminsa domin neman tsayawa takarar gwamna a Jihar Oyo. Wasikar murabus ɗinsa ta kawo ƙarshen jita-jitar da ke yawo, musamman bayan ya wuce wa’adin ranar 31 ga Maris da Shugaba Bola Tinubu ya bai wa masu rike da mukaman siyasa su yi murabus idan za su tsaya takara. 2. Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa tsohon Ministan Kudi, Wale Edun, da tsohon Ministan Gidaje, Ahmed Musa Dangiwa, sun yi murabus da kansu daga Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (FEC), ba wai an kore su ba. Mai magana da yawun…

Read More

Wata tankar man fetur (PMS) ta kife a Gadar Tincan Liverpool da ke Apapa, Jihar Lagos, lamarin da ya janyo mutane suka rika debar man da ya zube daga karkashin gadar. Tashar Channels Television ta wallafa bidiyon faruwar lamarin a safiyar ranar Litinin, inda aka ga wasu ‘yan Najeriya na kwasar man fetur daga tankar da ta kife, duk da hadarin da ke tattare da hakan. A cewar rahoton Channels TV: “Abin da ke faruwa a yanzu a Gadar Tincan Liverpool, Apapa: Tankar mai ta kife, mutane kuma suna dibar man da ya zube daga karkashin gadar.” Jaridar DAILY POST ta bayyana cewa fashewar tankokin mai na ci gaba da zama babbar…

Read More

Labaran Najeriya Na Yau – 5 Ga Junairu, 2026 1. Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta bayyana cewa mutane 25 sun mutu, yayin da 14 suka ɓacesakamakon hatsarin kwale-kwale da ya faru a ƙaramar hukumar Nguru ta Jihar Yobe. NEMA ta ce an ceto mutane 13 bayan hatsarin da ya faru da misalin ƙarfe 7:48 na yammacin Asabar. 2. Masu garkuwa da mutane da suka sace ‘yan’uwa biyu, Ibrahim da Tahir Abu, a Auchi da ke ƙaramar hukumar Etsako West, sun nemi kuɗin fansa har Naira miliyan 200. Mahaifinsu, Momoh Tahir, ya ce masu garkuwar sun tuntubi iyali da safiyar Lahadi domin neman…

Read More

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta JTF sun samu nasarar daƙile wani hari da ƴan bindiga suka tsara kai wa wasu garuruwa a ƙaramar hukumar Shanono da ke jihar Kano da ke arewacin Najeriya, bayan musayar wuta da aka shafe tsawon lokaci ana yi. Musayar wutar wadda aka fara tun cikin daren alhamis har zuwa wayewar safiyar juma’ar nan, ta afku ne a Yankwada da Babanduhu da sauran ƙauyuka da ke maƙotaka da yankin. Da yake tabbatar da lamarin ga kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN, mai magana da yawun rundunar a Kano, Major Zubair Babatunde, ya ce ƴan bindigar sun tsara…

Read More