Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 23, Oct. 2025

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 23, Oct. 2025

By Ahmad Habib IbrahimOktoba 23, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Labaran Najeriya Na Yau – 23 Ga Oct, 2025

1. Shari’ar Nnamdi Kanu:

Shugaban haramtacciyar kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, ya kammala tattaunawar sirri da tawagar lauyoyinsa karkashin jagorancin tsohon Babban Lauyan Tarayya, Kanu Agabi. Ana sa ran fara kare kansa a kotu ranar Alhamis, 23 ga Oktoba.

2. Zaben Shugaban Jam’iyyar PDP:

Shugabannin PDP daga Arewa, ciki har da gwamnoni, sun amince da tsohon Ministan Harkokin Musamman, Tanimu Turaki, a matsayin dan takarar hadin kai don kujerar shugaban jam’iyyar a babban taron da za a gudanar a watan Nuwamba.

3. Akpabio Ya Yaba Da Zabukan Najeriya:

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce tsarin zabe a Najeriya ya inganta sosai tun bayan ficewar PDP daga mulki. Ya bayyana haka ne yayin tattauna da majalisa kan kudirin gyaran dokar zabe a jiya Laraba.

4. ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aikinta:

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU ta dakatar da yajin aikin makonni biyu da ta fara. Shugaban ASUU na kasa, Farfesa Chris Piwuna, ne ya sanar da hakan a taron manema labarai a Abuja.

5. Gwamnan Jihar Neja Ya Yi Gargaɗi Ga ‘Yan Fashi:

Gwamna Mohammed Bago ya ce ba zai taba tattaunawa da ‘yan fashi ko biyan kudin fansa ba, ya kuma bukaci jama’a su kare kansu daga hare-haren da ake kai musu. Ya bayyana haka ne yayin ziyarar ta’aziyya ga mutanen Rijau da Magama.

6. Barazanar ISWAP:

Gwamnatocin jihohin Ondo da Kogi sun ce babu dalilin fargaba bayan gargadin DSS kan yiwuwar harin ISWAP a wasu yankunan jihohin. Sun ce jami’an tsaro suna cikin shiri don kare rayuka da dukiyoyi.

7. Farashin Naira:

Naira ta karu zuwa ₦1,492 kan kowanne dala a kasuwar bayan fage, daga ₦1,495 a jiya Talata. Sai dai ta fadi zuwa ₦1,462 a kasuwar musayar kudade ta NFEM.

8. Kananan Gwamnatocin Kano:

Mutane 500 daga jam’iyyar NNPP a Fagge da Ungogo sun koma jam’iyyar APC. Daraktan Hadejia-Jam’are River Basin, Rabiu Bichi, ne ya karɓe su jiya Laraba.

9. Jam’iyyar ADC Ta Kori Wasu Jiga-jiganta:

Rukunin ADC na jihar Kaduna ya kori mataimakin shugaban jam’iyyar na jiha, Ahmed Tijani Mustapha, da wasu mutum takwas saboda zargin aikata manyan laifuka.

10. Davido Ya Zama Shugaban Hukumar Wasanni:

Gwamnatin Osun ta nada shahararren mawaki David Adeleke (Davido) a matsayin shugaban Osun Sports Trust Fund, don taimakawa wajen samo kudade da inganta harkokin wasanni a jihar.

Ilimi Labaran Najeriya Labaran Safiyar Yau Siyasa Tattalin Arziki tsaro WASANNI
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Tsohon Shugaban Kotun Da’a, Danladi Umar, Ya Shiga Gidan Yari Na Kuje

Yuli 9, 2026

Matsananciyar Yunwa A Arewacin Najeriya Ya Tayar Da Hankula

Yuli 9, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 7, Yuli. 2026

Yuli 7, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Tsohon Shugaban Kotun Da’a, Danladi Umar, Ya Shiga Gidan Yari Na Kuje
  • Matsananciyar Yunwa A Arewacin Najeriya Ya Tayar Da Hankula
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 7, Yuli. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 29, Yuni. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 25, Yuni. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.