Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 26, Mayu. 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 26, Mayu. 2026

By Ahmad Habib IbrahimMayu 26, 2026No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

1. Kotu za ta yanke hukunci kan cancantar Jonathan a zaben 2027

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja za ta yanke hukunci yau kan karar da ke neman hana Goodluck Jonathan tsayawa takarar shugaban kasa a 2027. Mai shari’a Peter Lifu zai kuma yanke hukunci kan ko Jonathan zai iya sake rantsuwa bayan ya taba yin hakan sau biyu kafin barin mulki a 2015.

2. INEC ta daukaka kara kan soke jadawalin zaben 2027

Independent National Electoral Commission ta daukaka kara kan hukuncin da ya soke sabon jadawalin zabukan 2027 da ta fitar.

3. Atiku ya kalubalanci kuri’un Tinubu a zaben APC

Atiku Abubakar ya yi watsi da ikirarin cewa Bola Ahmed Tinubu ya samu kuri’u sama da miliyan 10 a zaben fidda gwani na APC.

4. Sojoji sun gargadi jama’a kan yiwuwar hare-haren ta’addanci lokacin Babbar Sallah

Rundunar sojin Najeriya ta gargadi jama’a kan yiwuwar hare-haren Boko Haram da ISWAP a yankunan Arewa maso Gabas yayin bikin Eid-el-Kabir.

5. Wike ya yi magana kan janyewar Fubara daga takarar APC

Nyesom Wike ya ce bai yi mamakin janyewar Siminalayi Fubara daga zaben fidda gwamnan APC a Rivers ba.

6. Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutun Babbar Sallah

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Laraba 27 da Alhamis 28 ga Mayu, 2026 a matsayin ranakun hutun Eid-ul-Adha.

7. Sanata Shehu Umar ya fice daga APC zuwa PRP

Sanata Shehu Umar mai wakiltar Bauchi ta Kudu ya fice daga APC tare da komawa jam’iyyar PRP saboda rashin adalci da dimokuradiyya a cikin jam’iyyar.

8. ’Yan bindiga sun kai hari fadar sarki a Kwara

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai hari garin Yashikira a Kwara inda suka kona wani bangare na fadar sarki tare da yin garkuwa da matan sarkin uku da yara hudu.

9. Ghana ta kama ’yan Najeriya takwas a samame

Rundunar ’yan sandan Ghana ta kama ’yan Najeriya takwas tare da wasu mutane 66 a wani samame kan safarar miyagun kwayoyi da sauran laifuka.

10. Tsohon Sufeto Janar na ’yan sanda ya fice daga APC

Tsohon Sufeto Janar na ’yan sanda, Mohammed Adamu, ya yi murabus daga APC saboda burinsa na takarar gwamnan 2027.

Labaran Safiyar Yau
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 25, Mayu. 2026

Mayu 25, 2026

‘No Means No’ — Mutanen Greenland Sun Yi Zanga-zanga Kan Trump

Mayu 22, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Jumaʼa 22, Mayu. 2026

Mayu 22, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 26, Mayu. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 25, Mayu. 2026
  • ‘No Means No’ — Mutanen Greenland Sun Yi Zanga-zanga Kan Trump
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Jumaʼa 22, Mayu. 2026
  • Shugabar Hukumar Wutar Lantarki ta Nijar, Fati Abarchi, ta kai ziyara zuwa manyan cibiyoyin samar da wutar lantarki a birnin Niamey
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.