Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 06, Oct. 2025

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 06, Oct. 2025

By Ahmad Habib IbrahimOktoba 6, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Labaran Najeriya Na Yau – 06 Ga Oct, 2025

  1. NDLEA ta kama manyan dillalan kwaya a Legas
    Hukumar NDLEA ta lalata manyan kungiyoyin dillalan miyagun kwayoyi guda biyu da ke da hannu a jigilar kwayoyi guda shida na cocaine a Legas. Hukumar ta kama mutane biyar, ciki har da shugaban kungiyar, Alhaji Hammed Taofeek Ode.
  2. Ministan Wuta, Adelabu, ya ce lokaci ya yi da zai zama Gwamnan Oyo
    Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa zai tsaya takarar gwamnan Jihar Oyo a 2027, yana mai cewa “lokacinsa ne yanzu.”
  3. ‘Yan bindiga sun kashe mutane biyu a Bwari, Abuja
    Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kashe mutane biyu a Bwari yayin da suke dawowa daga bikin aure daga Gwagwalada.
  4. Jam’iyyar ADC ta soki Shugaba Tinubu kan tsaro
    Jam’iyyar ADC ta zargi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da rashin kula da matsalar tsaro a ƙasar, tana mai cewa yana fifita siyasa sama da rayukan ‘yan ƙasa.
  5. Wike da Fubara sun gana da dattawan Rivers
    Ministan Abuja, Nyesom Wike, da Gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara, sun gana da dattawan jihar a Port Harcourt domin tattauna rikicin siyasar jihar.
  6. Oshiomhole ya gargadi Jonathan da kada ya tsaya takara
    Tsohon Gwamnan Edo, Adams Oshiomhole, ya gargadi tsohon Shugaba Goodluck Jonathan da kada ya sake shiga takarar shugaban ƙasa a 2027, yana cewa hakan zai lalata tarihinsa.
  7. NDLEA ta ƙone tan 24,897 na tabar wiwi a Edo da Osun
    Hukumar ta lalata sama da 24,000kg na skunk a dazukan Edo da Osun, inda ta kuma gano gona hudu da ake nomanta.
  8. ’Yan sanda sun kama ’yan kungiyar asiri biyar a Badagry
    Rundunar ’yan sanda a Legas ta kama mutane biyar bayan fafatawar kungiyoyin asiri a yankin Onireke da Isashi, Badagry.
  9. Sojoji sun karyata labarin cewa ‘yan bindiga sun kwace musu makamai a Kwara
    Rundunar sojojin Najeriya ta ce labarin da ke yawo cewa ‘yan bindiga sun karbe musu makamai da harsasai a Kwara ƙarya ne.
  10. Imisi ta lashe gasar Big Brother Naija (Season 10/10)
    Jarumar fim da mai zanen kaya, Imisioluwa Ayanwale (Imisi), ta zama zakarar gasar BBNaija ta bana, inda ta samu kyautar Naira miliyan 80, SUV da sauran lada.

Labaran Safiyar Yau
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Juma’a 5, Yuni, 2026

Yuni 5, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 4, Yuni. 2026

Yuni 4, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 3, Yuni. 2026

Yuni 3, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Juma’a 5, Yuni, 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 4, Yuni. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 3, Yuni. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 2, Yuni. 2026
  • Role Din Adam Zango Ne Aka Bawa Jarumin – Ahmad Editer
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.