Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 6, Nov. 2025

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 6, Nov. 2025

By Ahmad Habib IbrahimNuwamba 6, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Labaran Najeriya Na Yau –6 Ga Nov, 2025

Majalisar Dattawa ta nuna damuwa kan asarar man fetur da ake zargin Najeriya ta yi fiye da dala biliyan $300saboda sata da rashin tsari a yankin Neja-Delta. Rahoton wucin gadi na kwamiti ƙarƙashin Sanata Ned Nwoko ya bayyana hakan.

Bangaren PDP na Nyesom Wike ya soke taron gangamin jam’iyyar na kasa, bisa hujjar cewa ci gaba da shiryawa zai sabawa hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

Shugaban Sojin Sama, Air Marshal Sunday Aneke, ya kira dukkan kwamandojin rundunar sojin sama don ba su sabbin umarni kan yaƙi da ta’addanci a fadin ƙasar.

Majalisar Dattawa ta dakatar da tabbatar da Kingsley Udeh a matsayin minista saboda babu takardar tsaron sirridaga hukumomin leƙen asiri.

Majalisar Dattawa ta amince da dokar da ke hukunta malamai da ke lalata da ɗalibai da ɗaurin shekara 14 a kurkuku. Dokar na nufin dakatar da cin zarafin ɗalibai musamman mata a jami’o’i.

Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirinta na sayar da matatun mai na Warri, Port Harcourt da Kaduna domin jawo jarin waje da ƙarfafa gasa a masana’antar mai.

Kungiyar ’Yan Kwangila na Gida (All Indigenous Contractors Association) ta gudanar da zanga-zangar lumana a Majalisar Dokoki, tana neman a biya su kuɗaɗen ayyukan da suka kammala.

Gwamna Charles Soludo na Anambra ya karyata ikirarin cewa Kiristoci na Kudu maso Gabas na fuskantar kisan kare dangi na addini, yana cewa matsalar ta samo asali ne daga siyasa da tattalin arziki.

Hukumar NDLEA ta gargadi jama’a kan magungunan ƙarya da ake siyarwa a matsayin “cannabis mai magani.”Hukumar ta kama wani shahararren dillali Afeez Salisu a Mushin, Legas.

Kotun Tarayya a Legas ta hana ’yan sanda kama ko tsoratar da Omoyele Sowore, yayin da wata kotu a Abuja ta ƙi bayar da umarnin kama shi a shari’ar da DSS ke yi masa.

Labaran Safiyar Yau Majalisar Dattawa NDLEA PDP Soludo Sowore tinubu wike
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN

Yuli 20, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026

Yuli 16, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026

Yuli 15, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026
  • Tsohon Ministan Kimiyya, Uche Nnaji ya musanta zargin ƙirƙirar takardun shaidar karatu
  • Gwamnatin Tarayya ta dakatar da ƙarin kuɗin jarabawar WAEC da NECO bayan suka
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.