Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 17 a Arewa-Maso-Gabas

Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 17 a Arewa-Maso-Gabas

By Ahmad Habib IbrahimAgusta 5, 2025No Comments1 Min Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Rundunar sojin Najeriya ta sanar da nasarar kashe ‘yan ta’adda 17 na Boko Haram a wata gagarumar fafatawa da ta gudana a yankunan jihohin Borno da Adamawa. Wannan matakin yana daga cikin kokarin gwamnati na kawo karshen ta’addanci a yankin Arewa-Maso-Gabas da ya daɗe yana fama da rikici.

A cewar kakakin rundunar, an kaddamar da wannan farmaki ne bayan samun bayanan sirri da suka tabbatar da kasancewar wasu ‘yan Boko Haram a wasu maboya. An kuma kwato makamai, harsasai, da abinci da ‘yan ta’addan ke amfani da su.

An gudanar da wannan samame ne tare da hadin gwiwar jami’an Operation Hadin Kai, inda aka kai hari a maboyar da ke kusa da garuruwan Madagali da Damboa.

Rundunar sojin ta bayyana cewa wannan nasara wata alama ce da ke nuna cewa rikicin na karasa da kuma cewa rundunar za ta ci gaba da aikin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a yankin.

“Za mu ci gaba da murkushe ‘yan ta’adda a ko’ina suke. Rundunar sojoji ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya,” in ji kakakin rundunar.

Arewa Maso Gabas Boko haram Operation Hadin Kai Sojojin Najeriya tsaro
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN

Yuli 20, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026

Yuli 16, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026

Yuli 15, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026
  • Tsohon Ministan Kimiyya, Uche Nnaji ya musanta zargin ƙirƙirar takardun shaidar karatu
  • Gwamnatin Tarayya ta dakatar da ƙarin kuɗin jarabawar WAEC da NECO bayan suka
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.