Dakarun rundunar sojin Najeriya ta 8 Division, tare da hadin gwiwar 1 Brigade Combat Team da sauran rundunonin tallafi, sun kaddamar da wani samame kan ‘yan ta’adda a karamar hukumar Shinkafi da ke jihar Zamfara.
Wani masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi, Zagazola Makama, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafin X.
A cewarsa, an fara wannan samame da misalin karfe 9:00 na safe a ranar 4 ga Mayu, inda aka kai hari kan wuraren da aka gano ‘yan ta’addan suna boyewa a kauyukan Kamara, Dan Gwandi, Manawa da Katsira.
Ya kara da cewa dakarun sojin sun yi arangama da ‘yan ta’addan a kauyen Katsira, inda aka yi musayar wuta mai tsanani.
Rahotanni sun nuna cewa an kashe ‘yan ta’adda da dama a yayin wannan farmaki.
Sai dai kuma, sojoji uku sun samu raunukan harbin bindiga yayin wannan arangama, kuma a halin yanzu suna karbar kulawar likitoci.
A cewar sa:
“An tilasta wa ‘yan ta’addan janyewa daga yankin, inda suka tsere zuwa yankin tsaunukan Fakai sakamakon matsin lambar sojoji.”
Ya kara da cewa dakarun sojin na ci gaba da rike iko a yankin, yayin da ake kokarin korar sauran ‘yan ta’addan da suka tsere domin hana su sake samun damar motsi.
