AREWA24, tashar talabijin da ke kan gaba wajen yaɗa shirye-shirye masu nishaɗantar da iyali da tsarin rayuwa cikin harshen Hausa, wadda ke da ofishin samar da shirye-shirye a Najeriya da yammacin Afirka, ta shigar da ƙarar neman diyar naira biliyan goma, bisa zargin ɓata suna a kan Alhaji Ahmed Tijjani Ramalan, da kamfanin Atar Communications Nigeria Limited (masu gudanar da Liberty TV da Radio), da kuma Ƙungiyar Masu Kafofin Yaɗa Labarai na Arewa (NBMOA), biyo bayan wasu jerin zarge-zarge na karya, masu illa, kuma marasa tushe da aka yi wa kamfanin.


Matakin na shari’a, wanda aka shigar a gaban Babban Kotun Jiha da ke Jalingo, na neman a biya diyya kan taɓa martabar kamfanin da kuma asarar kuɗi da ya tafka sakamakon kalaman da ake zargin Ƙungiyar Masu Kafofin Yaɗa Labarai na Arewa (NBMOA), da Tijjani Ramalan sun fitar, waɗanda AREWA24 ta tabbatar cewa kalamai ne na yaudara, kuma suna da illa ga kimar da aka san kamfanin da ita, da kuma ayyukansu. Kamfanin ya jaddada cewa wadannan maganganu ba su da wani tushe na gaskiya, kuma akwai yiwuwar su lalata aminci da yarda da kamfanin ya gina tsakaninsa da masu kallon tashar, da abokan hulda, da masu ruwa da tsaki tsawon shekaru.
A cikin wani jawabi da ya fitar, kamfanin AREWA24 ya jaddada kudirinsa na kiyaye matakai na ƙwarewa, gaskiya, da shirye-shirye masu nagarta. “Mun gina martabarmu ne bisa shirye-shiryen nishadi masu inganci, wadanda suka dace da al’adu kuma suke da tasiri ga miliyoyin masu kallo a Najeriya, da yammacin Nahiyar Afirka da ma sauran sassa na duniya. Ba za mu taɓa barin duk wasu zarge-zarge marasa tushe daga wasu “gurbatattun” mutane su lalata yarda da kyakkyawar alaƙar da muka kafa ba,” in ji kamfanin.
AREWA24 ta ƙara da cewa, yayin da take maraba da sukar da za ta kawo ci gaba, za ta dauki dukkan matakan shari’a da suka dace don kare mutuncinta, ma’aikatanta, da muradun kasuwancinta. Kamfanin ya nuna kwarin gwuiwa kan tsarin shari’a sannan ya sake jaddada jajircewarsa a kan nuna gaskiya da amana.
Baya ga sauran bukatu, ƙarar na neman a biya diyar kudi har naira biliyan goma, da janye kalaman bata suna da aka yi a bainar jama’a, da kuma bayar da hakuri a hukumance daga Ahmed Tijjani Ramalan, da Atar Communications Nigeria Limited da kuma ƙungiyar NBMOA.
AREWA24 na ci gaba da gudanar da ayyukanta a matsayin daya daga cikin manyan kafafen yada labarai na talabijin da samar da shirye-shirye a yankin Sahara na Afirka, da yaɗa ingantattun shirye-shirye masu nishaɗantarwa da ilimantarwa da aka tsara musamman domin ɗimbin masu kallonta daga bangarori daban-daban.

Leave a Reply
You must be logged in to post a comment.