Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 29, Yuni. 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 29, Yuni. 2026

By Ahmad Habib IbrahimYuni 29, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Takaitattun Labaran NajeriyaAa Yau Litinin

1. Gwamnati ta gargadi masu sayar da fetur kan rage farashi
Hukumar FCCPC ta nuna damuwa cewa duk da faduwar farashin danyen mai a kasuwar duniya, farashin fetur a Najeriya bai ragu yadda ya kamata ba. Hukumar ta yi gargadin cewa za ta binciki duk wani kamfani da aka samu yana cutar da masu amfani.

2. Gwamnatin Katsina ta yi magana kan zargin kama shugabannin ‘yan bindiga
Gwamnatin Jihar Katsina ta ce ba za ta yi tsokaci ba kan rahotannin da ke cewa an kama wasu da ake zargin shugabannin ‘yan bindiga ne bayan dawowarsu daga aikin Hajjin 2026, tana mai cewa lamarin yana hannun hukumomin tsaro na tarayya.

3. An ce ‘yan bindiga sun dasa bam a Sokoto
Mazauna garuruwan Kurawa da kewaye sun yi zargin cewa ‘yan bindiga sun dasa bam na IED a hanyar Sabon Birni–Kurawa domin hana jami’an tsaro kai dauki yayin hare-hare.

4. Seriake Dickson ya ce APC za ta sha kaye a 2027
Jagoran jam’iyyar NDC, Sanata Seriake Dickson, ya bayyana cewa idan aka gudanar da zaben 2027 cikin gaskiya da adalci, Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC za su fadi zabe saboda rashin gamsuwar jama’a.

5. Rundunar Sojin Ruwa ta dakile safarar haramtaccen mai
Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya ta ce ta lalata wata hanyar safarar haramtaccen man fetur a jihar Rivers, bayan wani samame da ta kai a karkashin Operation DELTA SENTINEL.

6. Kudirin kafa ‘yan sandan jihohi ya shiga sabon mataki
Majalisar Tarayya za ta tura kudirin gyaran kundin tsarin mulki na kafa ‘yan sandan jihohi zuwa majalisun dokokin jihohi 36 domin su kada kuri’a. Ana bukatar aƙalla jihohi 24 su amince kafin kudirin ya zama doka.

7. ‘Yan sanda sun kama mutane bakwai a Ogun
Rundunar ‘yan sandan Ogun ta kama mutane bakwai da ake zargi da laifukan fashi da makami, “one chance”, kungiyar asiri da damfara. An kuma kwato motoci, bindigogi, wayoyi 17, kwamfuta da kuma sama da Naira miliyan 1.1.

8. Kwankwaso ya ce ana kara hada kan NDC
Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar NDC, Rabiu Kwankwaso, ya ce ana kokarin kara hada kan jam’iyyar da shirya ta domin zaben shekarar 2027.

9. APC ta karyata jerin sunayen da ke yawo a intanet
Jam’iyyar APC ta bayyana cewa jerin sunayen wadanda ake cewa sun lashe zabukan fidda gwani da ke yawo a kafafen sada zumunta ba na hukuma ba ne, tare da gargadin jama’a kada su amince da su.

10. An haramta babura da adaidaita sahu a hanyar Lagos-Calabar
Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya ta sanar da haramta zirga-zirgar babura da adaidaita sahu a babbar hanyar Lagos-Calabar Coastal Highway, kuma dokar za ta fara aiki daga wannan makon.

Labaran Safiyar Yau
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 25, Yuni. 2026

Yuni 25, 2026

Bayan Watanni 6 a Tsare, Kotu Ta Sanya Ranar Fara Shari’ar Dan Jarida Olayinka

Yuni 25, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 22, Yuni, 2026

Yuni 22, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 29, Yuni. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 25, Yuni. 2026
  • Bayan Watanni 6 a Tsare, Kotu Ta Sanya Ranar Fara Shari’ar Dan Jarida Olayinka
  • Firaministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus Bayan Matsin Lambar Siyasa
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 22, Yuni, 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.