Tag: Labaran Safiyar Yau

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 23, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 23 Ga Oct, 2025

    1. Shari’ar Nnamdi Kanu:

    Shugaban haramtacciyar kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, ya kammala tattaunawar sirri da tawagar lauyoyinsa karkashin jagorancin tsohon Babban Lauyan Tarayya, Kanu Agabi. Ana sa ran fara kare kansa a kotu ranar Alhamis, 23 ga Oktoba.

    2. Zaben Shugaban Jam’iyyar PDP:

    Shugabannin PDP daga Arewa, ciki har da gwamnoni, sun amince da tsohon Ministan Harkokin Musamman, Tanimu Turaki, a matsayin dan takarar hadin kai don kujerar shugaban jam’iyyar a babban taron da za a gudanar a watan Nuwamba.

    3. Akpabio Ya Yaba Da Zabukan Najeriya:

    Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce tsarin zabe a Najeriya ya inganta sosai tun bayan ficewar PDP daga mulki. Ya bayyana haka ne yayin tattauna da majalisa kan kudirin gyaran dokar zabe a jiya Laraba.

    4. ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aikinta:

    Kungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU ta dakatar da yajin aikin makonni biyu da ta fara. Shugaban ASUU na kasa, Farfesa Chris Piwuna, ne ya sanar da hakan a taron manema labarai a Abuja.

    5. Gwamnan Jihar Neja Ya Yi Gargaɗi Ga ‘Yan Fashi:

    Gwamna Mohammed Bago ya ce ba zai taba tattaunawa da ‘yan fashi ko biyan kudin fansa ba, ya kuma bukaci jama’a su kare kansu daga hare-haren da ake kai musu. Ya bayyana haka ne yayin ziyarar ta’aziyya ga mutanen Rijau da Magama.

    6. Barazanar ISWAP:

    Gwamnatocin jihohin Ondo da Kogi sun ce babu dalilin fargaba bayan gargadin DSS kan yiwuwar harin ISWAP a wasu yankunan jihohin. Sun ce jami’an tsaro suna cikin shiri don kare rayuka da dukiyoyi.

    7. Farashin Naira:

    Naira ta karu zuwa ₦1,492 kan kowanne dala a kasuwar bayan fage, daga ₦1,495 a jiya Talata. Sai dai ta fadi zuwa ₦1,462 a kasuwar musayar kudade ta NFEM.

    8. Kananan Gwamnatocin Kano:

    Mutane 500 daga jam’iyyar NNPP a Fagge da Ungogo sun koma jam’iyyar APC. Daraktan Hadejia-Jam’are River Basin, Rabiu Bichi, ne ya karɓe su jiya Laraba.

    9. Jam’iyyar ADC Ta Kori Wasu Jiga-jiganta:

    Rukunin ADC na jihar Kaduna ya kori mataimakin shugaban jam’iyyar na jiha, Ahmed Tijani Mustapha, da wasu mutum takwas saboda zargin aikata manyan laifuka.

    10. Davido Ya Zama Shugaban Hukumar Wasanni:

    Gwamnatin Osun ta nada shahararren mawaki David Adeleke (Davido) a matsayin shugaban Osun Sports Trust Fund, don taimakawa wajen samo kudade da inganta harkokin wasanni a jihar.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 22, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 22 Ga Oct, 2025

    1. An ƙona sakatariyar jam’iyyar ADC a Ado-Ekiti

    Wasu da ake zargin ’yan daba ne suka ƙona sakatariyar jam’iyyar ADC da ke yankin Basiri, Ado-Ekiti a daren Litinin. Wuta ta lalata kujeru, kayan ofis, lasifika da sauran kayan aiki.

    2. Kotu ta soke zaɓen kananan hukumomi a Ebonyi

    Babbar kotun tarayya da ke Abakaliki ta soke zaɓen kananan hukumomi da aka gudanar a watan Yuli 2024 a Jihar Ebonyi. Mai shari’a Hillary Oshomah ya ce zaɓen bai bi tanadin dokar zaɓe ba.

    3. Gobarar mota mai ɗauke da fetur ta kashe mutane a Neja

    Mutane da dama sun mutu a mummunar fashewar tankar mai da ta faru a hanyar Agaie–Bida, kusa da Essa, a ƙaramar hukumar Katcha, Jihar Neja. Gobarar ta haddasa cunkoson ababen hawa sosai.

    4. Tinubu ya nada sabon Minista daga Jihar Plateau

    Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Dr Bernard Mohammed Doro daga Jihar Plateau a matsayin Minista. Nadinsan na jiran amincewar majalisar dattawa kafin ya fara aiki.

    5. Gwamna Bala Mohammed ya kafa sabbin masarautu 13 a Bauchi

    Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed, ya rattaba hannu kan dokar da ta ƙirƙiri sabbin masarautu 13 da sarakuna 111 a faɗin jihar. Haka kuma ya soke dokar Sayawa Chiefdom tare da kafa Zaar Chiefdom da hedkwata a Mhrim Namchi.

    6. Lauyan Nnamdi Kanu da ’yan uwansa sun shiga gidan yari

    Wata kotun majistare a Kuje ta bayar da umarnin tsare lauya Aloy Ejimakor, ɗan’uwan Nnamdi Kanu, da wasu mutum 10 da aka kama a zanga-zangar #FreeNnamdiKanu.

    7. Kotun Koli ta dakatar da yanke hukunci kan karar PDP da Tinubu

    Kotun koli ta ɗage yanke hukunci a kan karar da jihohin da jam’iyyar PDP ke mulki suka shigar don kalubalantar ayin dokar ta baci da Shugaba Tinubu ya ayyana a Jihar Rivers.

    8. Gwamnati ta umarci MDAs su mika asusun su na bankuna

    Ofishin Akanta Janar na Tarayya ya umarci dukkan Ma’aikatu, Hukumomi da Sassa (MDAs) su mika bayanan asusun su da ke bankunan kasuwanci, domin inganta tsarin kula da kuɗi.

    9. Dan majalisa Ojema Ojotu ya sauya sheka daga PDP zuwa APC

    Dan majalisar wakilai mai wakiltar Apa/AgatuOjema Ojotu, ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC. Mataimakin Kakakin Majalisa, Benjamin Kalu, ne ya karanta wasikar sauya shekar a zaman majalisar.

    10. INEC ta ce masu kada kuri’a miliyan 2.8 za su shiga zaɓen Anambra

    Hukumar zaɓe ta ƙasa, INEC, ta ce kimanin miliyan 2.8 na masu kada kuri’a ne za su shiga zaɓen gwamnan Anambra da za a gudanar a 8 ga Nuwamba, 2025.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 16 Ga Oct, 2025

    1. Majalisar Dattawa za ta fara tantance Farfesa Joash Ojo Amupitan, SAN, a yau Alhamis, wanda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC). Daraktan bayanai na Ofishin Sakatare na Majalisar Dokoki, Bullah Audu Bi-Allah, ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa ranar Laraba.

    2. Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, ya yi murabus daga jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP). Kakakinsa, Daniel Alabrah, ne ya bayyana hakan, amma bai fayyace dalilin ficewarsa daga jam’iyyar ba.

    3. Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce gwamnoni na jam’iyyar PDP da suka koma jam’iyyar APC ya kamata su gode masa. Wike ya ce kyawawan ayyukansa ne suka ba su damar yin hakan, kuma hakan ya tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba Bola Tinubu.

    4. Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama wasu tsoffin jami’anta da aka kora, bisa zargin amfani da sunan hukumar wajen aikata zamba. Hukumar ta bayyana hakan a wata sanarwa ranar Laraba, inda ta ce waɗanda aka kama—Barry Donald da Victor Godwin—za a gurfanar da su a kotu.

    5. Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bayyana cewa canjin jam’iyya da wasu gwamnoni suka yi zuwa APC ya tabbatar da matsayar da hadakar jam’iyyun adawa suka dauka cewa ana ƙoƙarin maida Najeriya jam’iyya ɗaya. A wata sanarwa, mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Mallam Bolaji Abdullahi, ya ce jam’iyyarsu ba ta damu da abin da ya kira “rashin aminci na siyasa” daga gwamnoni ba.

    6. Sanata Seriake Dickson, wanda ke wakiltar Bayelsa ta Yamma, ya bayyana adawarsa ga yawaitar ficewar ‘yan siyasa zuwa jam’iyyar APC. Yayin da yake magana da ‘yan jarida a Majalisar Dokoki ta Ƙasa a Abuja ranar Laraba, bayan zaman majalisa, Dickson ya ce yana nan daram a PDP.

    7. Tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan ya koka da yadda aka bar manyan ayyukan da ya fara lokacin da yake Gwamnan Jihar Bayelsa, yana zargin gwamnatocin da suka biyo baya da rashin ci gaba da tsare-tsarensa na cigaba. Yayin kaddamar da otal ɗin Best Western Plus Hotel a Yenagoa ranar Laraba, Jonathan ya ce ya fara gina wasu otal-otal domin jawo zuba jari da yawon bude ido a jihar kafin ya zama mataimakin shugaban ƙasa a 2007.

    8. Babbar Kotun Jihar Kano, ƙarƙashin mai shari’a Musa Dahuru Muhammad, ta yanke wa wani kocin ƙwallon ƙafa, Hayatu Muhammad, hukuncin ɗaurin shekaru takwas a gidan yari ba tare da zabin biyan tara ba, saboda yin lalata da ƙaramin ɗan wasansa. An tabbatar da cewa wanda aka yanke wa hukuncin ya aikata laifin sau biyu a wurare daban-daban a yankin Dala.

    9. Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta ce ta ceto mutane uku da aka sace tare da kama mutane shida da ake zargi da hannu a satar, a ƙauyen Euga, ƙaramar hukumar Toro ta jihar. Mai magana da yawun rundunar, Ahmed Wakil, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa.

    10. Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya bayyana a ranar Laraba cewa ya ƙi karɓar mukamin gwamnati daga Shugaba Bola Tinubu, yana mai cewa yanzu yana son mayar da hankali kan rayuwarsa ta kashin kai bayan shekaru da dama a harkar siyasa. Fayose, wanda mamba ne na jam’iyyar PDP, ya ce duk da dangantakar sa ta kusa da Shugaba Tinubu, ba shi da niyyar shiga ko karɓar wani mukami a ƙarƙashin gwamnatin APC.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 15 Ga Oct, 2025

    1. Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, ya tafi ƙasar Birtaniya domin neman magani, kamar yadda wasu majiyoyi suka tabbatar a safiyar Talata. Rahoton ya ce ministan zai iya ci gaba da jinya a can idan likitoci suka ba da shawarar hakan.


    2. Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya, Super Eagles, ta lallasa ƙasar Benin da ci 4–0 a filin wasa na Godswill Akpabio da ke Uyo. Duk da wannan nasara, ba su samu tikitin kai tsaye zuwa gasar Copa Duniya ta 2026 ba, sai dai za su buga wasan tazarce (playoff) na ƙasashen Afirka.


    3. Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP, Kogi Central), ta bayyana cewa mata ’yan Najeriya da aka safarar zuwa Libya suna haihuwa a cikin gidajen yari. Ta bukaci hukumomin Shige da Fice da Kurkuku su hada kai da jami’an Libya domin dawo da waɗannan mata da ’ya’yansu gida Najeriya.


    4. Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa halin tattalin arziki zai inganta nan ba da jimawa ba, yana mai cewa kasar na shiga sabon mataki na ci gaban tattalin arziki. Ya bayyana haka a taron Nigeria Renewable Energy Innovation Forum (NREIF) da aka gudanar a Abuja, yana mai cewa Shugaba Bola Tinubu na jin radadin talakawa.


    5. Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dage sauraron karar da ke neman dakatar da taron gangamin jam’iyyar PDP har zuwa Alhamis, domin bangarorin biyu su sasanta rikicin lauyoyi. Alƙali Justice James Omotosho ne ya bayar da umarnin bayan rikici ya tashi tsakanin manyan lauyoyi Chris Uche (SAN) da Kamaldeen Ajibade (SAN) kan wanda ke wakiltar jam’iyyar PDP.


    6. Jam’iyyar APC ta yanke shawarar amfani da tsarin zabe na yarjejeniya (consensus) wajen zaɓen ɗan takararta na gwamna a jihar Ekiti don zaben 27 ga Oktoba. Wannan ya biyo bayan janyewar Mrs. Atinuke Omolayo, wanda ya bar Gwamna Biodun Oyebanji shi kaɗai a takara.


    7. Rundunar ’Yan Sandan Jihar Jigawa ta kama mutane 105 bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi a fadin jihar. Kakakin rundunar, SP Shi’isu Adam, ya tabbatar da hakan a lokacin da yake zantawa da ’yan jarida a Dutse ranar Talata.


    8. Majalisar Dattawa za ta tantance kuma ta tabbatar da Prof. Joash Amupitan a matsayin Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) yau Laraba, bayan wasikar da Shugaba Bola Tinubu ya aikewa majalisar ranar Talata.


    9. Majalisar Wakilai ta fara kokarin kawo karshen rikici tsakanin Gwamnatin Tarayya da kungiyar ASUU. Wannan ya biyo bayan kudirin da Sesi Oluwaseun Whingan, dan majalisa mai wakiltar Badagry, ya gabatar domin samar da mafita mai dorewa.


    10. Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya ce Gwamna Peter Mbah na Jihar Enugu yanzu shi ne jagoran jam’iyyar APC a jihar, bayan da ya koma jam’iyyar daga PDP ranar Talata. Ya bayyana hakan a lokacin taron maraba da shi a Okpara Square, Enugu.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 09, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 09 Ga Oct, 2025

    1. Bankin Duniya ya ce Najeriya ta tabbatar da sauyin tattalin arziki ya amfani talakawaBankin Duniya (World Bank) ya bukaci Najeriya da ta tabbatar da cewa sakamakon gyare-gyaren tattalin arziki da ake yi ya zama abin amfani ga jama’a. Shugaban Bankin Duniya a Najeriya, Mathew Verghis, ya bayyana cewa sama da mutane miliyan 139 na rayuwa cikin talauci a kasar, don haka gwamnati ta mayar da hankali wajen sauƙaƙa rayuwar jama’a.

    1. Sojoji sun ceto mutum 37 da aka yi garkuwa da suRundunar sojin Najeriya ta sanar da cewa dakarunta sun ceto mutum 37 da aka yi garkuwa da su a yayin wani babban farmaki kan ‘yan ta’adda. An kashe ‘yan ta’adda 9, an kama mutane 8, tare da kwace makamai da dama a cikin wannan samame.

    1. Naira ta kara karfi a kasuwaNaira ta karu zuwa ₦1,490/$1 a kasuwar bayan fage, daga ₦1,495/$1 a jiya. Haka kuma a kasuwar musayar kudade ta gwamnati (NFEM), Naira ta karu zuwa ₦1,469/$1, bisa rahoton tattalin arziki na yau Laraba.

    1. Akpabio da Abba Moro sun yi takaddama a Majalisar DattawaShugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, da Jagoran ‘Yan adawa, Sanata Abba Moro, sun yi gardama kan yawaitar sauya sheka daga jam’iyyun adawa zuwa APC. Akpabio ya ce rashin tsari a jam’iyyun adawa ne ke sa hakan, sai dai Moro ya mayar da martani cewa adawa za ta ci gaba da tsayawa da kafafunta komai rashi.

    1. Orji Kalu ya ce Tinubu zai sake lashe zabe a 2027Tsohon Gwamnan Abia, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai sake lashe zaben 2027, yana mai cewa babu wanda zai iya kayar da shi – ko Atiku AbubakarGoodluck Jonathan, ko Peter Obi.

    1. ’Yan sanda sun dakatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhuRundunar ’yan sanda ta dakatar da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (tinted glass permit) bayan an ba ta sammaci daga kotu. Mai magana da yawun rundunar FCT, Josephine Adeh, ce ta tabbatar da hakan a wani shirin talabijin.

    1. INTERPOL ta tabbatar da kama dan Najeriya da ya yi damfara ta soyayyaHukumar INTERPOL ta tabbatar da cewa jami’an tsaro a Argentina sun kama wani dan Najeriya mai suna Ikechukwu N., wanda ake zargi da shirya damfara ta yanar gizo ta hanyar soyayya wadda ta shafi mata dubban a kasashe daban-daban.

    1. Wike ya gargadi shugaban AMAC kan sa suna kan tituna ba bisa ka’ida baMinistan FCT, Nyesom Wike, ya gargadi shugaban karamar hukumar AMACChristopher Maikalangu, da ya daina sanya sunaye a tituna da hanyoyi da ba tare da izini daga ma’aikatar babban birnin tarayya ba.

    1. Kotu ta jinkirta sauraron karar EFCC har zuwa Oktoba 9Wata kotu ta musamman a Ikeja ta dage shari’ar EFCC har zuwa ranar 9 ga Oktoba, domin ta yanke hukunci kan sahihancin hujjojin dijital da hukumar ta gabatar. Alkalin kotun, Justice Rahman Oshodi, ya ce ya bukaci karin lokaci don nazarin shaidun da aka gabatar.

    1. Kotu ta kara mako guda ga kwamitin likitoci don duba lafiyar Nnamdi KanuKotun Tarayya a Abuja ta bai wa kwamitin likitocin da ke duba lafiyar jagoran IPOBNnamdi Kanu, karin mako guda, bayan sun kasa kammala binciken lafiyarsa cikin kwanaki takwas da kotu ta diba a baya.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 08, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 08 Ga Oct, 2025

    1. Ministan Kirkira, Kimiyya da Fasaha, Geoffrey Uche Nnaji, ya yi murabus. Murabus ɗinsa a ranar Talata ya biyo bayan zargin bogin takardar shaidar karatu da ake yi masa.

    2. Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya sauka daga mukaminsa, wanda hakan ke nuna fara sabon shugabanci a hukumar. Yakubu, wanda aka rantsar a karo na biyu a ranar 9 ga Disamba, 2020, ya sanar da matakin nasa yayin taron da ya yi da kwamishinonin zaɓe na jihohi (RECs) a ranar Talata.

    3. Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta halarci zaman majalisa a karon farko a ranar Talata bayan kammala watanni shida na dakatar da ita saboda rashin da’a. A ranar 23 ga Satumba, jami’in tsaro na majalisar, Alabi Adedeji, ya buɗe ofishinta domin ba ta damar dawowa bayan dakatarwar. A lokacin zaman, Sanatar ta zauna a kujerarta da aka ware mata cikin jerin ‘yan adawa ba tare da wata matsala ba.

    4. Shugabannin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) sun gudanar da taro a ranar Talata. A yayin taron, shugaban jam’iyyar, David Mark, ya zargi ‘yan siyasa da kafa gwamnatoci da ke yi musu aiki kawai, yana mai cewa, “ya zama dole mu canza wannan tsohon salon. Dole mu nuna sabon hali na jagoranci a kowane fanni — gwamnati, kamfanoni, da al’umma.”

    5. Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai hari a garin Zhibi, kusa da Dei-Dei a Babban Birnin Tarayya, amma yana cikin ƙaramar hukumar Tafa ta Jihar Neja. An ce sun sace wani ɗan kasuwa mai suna Muhammad Shuaibu tare da ‘ya’yansa mata biyu — ɗaya ɗaliba ce a jami’a, ɗaya kuma ƙaramar ‘yar’uwarta ce.

    6. Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya nemi amincewar Majalisar Wakilai don ɗaukar sabon bashin ƙasashen waje da kuma sake biyan wasu tsoffin bashi da adadinsu ya kai dala biliyan 2.3. Haka kuma ya nemi amincewar fitar da takardar bashin sukuk ta farko ta ƙasar mai darajar dala miliyan 500 a kasuwar kuɗin duniya.

    7. Majalisar Dattawa ta bayyana a ranar Talata cewa Kamfanin Mai na Ƙasa (NNPC Limited) ya amsa tambayoyi 19 da aka yi masa a rahoton bincike daga 2017 zuwa 2023. Sai dai shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan asusun jama’a, Sanata Aliyu Wadada, ya ce har yanzu ba su kammala nazarin amsoshin ba.

    8. Tsofaffin ‘yan sanda da ke ƙarƙashin tsarin Contributory Pension Scheme sun ce za su ci gaba da zanga-zangar su a ranar 14 ga Oktoba a Majalisar Ƙasa, duk da matakan sulhu da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da Sufeto Janar na ‘Yan sanda suka ɗauka. Sun dade suna neman a cire su daga tsarin CPS kuma a kafa musu hukumar fansho ta musamman kamar yadda rundunar soja da DSS suke da ita.

    9. Hukumar NDLEA ta Jihar Edo ta ce ta kama mutane 54 da nauyin kayan maye mai nauyin kilo 1,506.57 a watan Satumba. A wata sanarwa da kwamandan hukumar, Mitchell Ofoyeju, ya fitar a ranar Talata, ya ce sun kuma lalata kilo 66,078.57 na tabar wiwi (skunk cannabis).

    10. Rundunar Sojan Najeriya ta 2 Brigade da ke Jihar Akwa Ibom ta la’anci kisan da aka yi wa Laftanar Samson Haruna, likitan soja na 6 Battalion, wanda ya mutu bayan matarsa ta ƙone shi saboda rikicin cikin gida a barikin Willington Bassey.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 07, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 07 Ga Oct, 2025

    1. Gwamnatin Tarayya ta soki kungiyar PENGASSAN kan yajin aiki
      Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya soki kungiyar ma’aikatan man fetur ta Najeriya (PENGASSAN) bisa yajin aikin da suka gudanar saboda sabani da Dangote Refinery. Tinubu ya ce ba za a bar ƙasa ta tsaya cik saboda matsalolin da za a iya warwarewa cikin tattaunawa ba.
    2. Za a gudanar da taron Majalisar Koli ranar Alhamis a Abuja
      Ofishin Sakatare Janar na Gwamnati (SGF), Sanata George Akume, ya tabbatar da cewa za a gudanar da taron Council of State a Abuja ranar Alhamis ta hanyar haɗa taron kai tsaye da na yanar gizo. Haka kuma za a gudanar da taron Majalisar ‘Yan Sanda a wannan rana.
    3. Wike: Tinubu yana samar da ayyukan yi ta hanyoyin Abuja
      Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa ayyukan gine-ginen hanyoyi da ake yi a Abuja suna taimaka wa matasa da samar da ayyukan yi. Ya kuma bukaci jama’a su biya haraji domin ci gaba da samar da kayayyakin more rayuwa.
    4. Tinubu ya bada umarni a sake nazarin kudin aikin Hajji 2026
      Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci hukumar aikin Hajji ta ƙasa (NAHCON) da ta sake nazarin farashin aikin Hajji na shekara ta 2026 cikin kwanaki biyu, domin rage wa maniyyata nauyin tafiya.
    5. Gobara ta tashi a ofishin gwamnati a Ribas
      Wani sashi na Rivers State Secretariat ya kama da wuta a safiyar Litinin. Shugabar ma’aikata ta jihar, Dr. Inyingi S. I. Brown, ta tabbatar da cewa babu wanda ya jikkata.
    6. Lauya ya roƙi kotu ta hana Jonathan tsayawa takara a 2027
      Lauya Johnmary Chukwukasi Jideobi ya shigar da kara a kotun tarayya da ke Abuja, yana neman a hana tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan tsayawa takara a zaben shugaban kasa na 2027. Ya kuma roƙi kotun ta hana INEC karɓar sunansa daga kowace jam’iyya.
    7. Dubban masu zanga-zanga sun mamaye Kaduna kan batun man fetur
      Dubban mutane karkashin Partners for National Economic Progress (PANEP) sun gudanar da zanga-zanga a Kaduna, suna zargin wasu manyan masu ruwa da tsaki da hana ci gaban masana’antar man fetur a cikin gida. Sun yi kira da a kare Dangote Refinery da kuma kawo ƙarshen masu shigo da man daga waje.
    8. PDP ta fara tattara jerin wakilai don babban taron ƙasa
      Jam’iyyar PDP ta fara tattara sunayen wakilan da za su halarci babban taron ƙasa da aka shirya gudanarwa a Ibadan, Jihar Oyo, a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba. Gwamnan Adamawa, Ahmadu Fintiri, ne ya tabbatar da hakan.
    9. ’Yan sanda sun kama mutum 153 a Jigawa
      Rundunar ’yan sanda ta jihar Jigawa ta sanar da kama mutum 153 da ake zargi da laifuka daban-daban, tare da kwace miyagun ƙwayoyi, kuɗi da babur. Mai magana da yawun rundunar, SP Shi’isu Adam, ne ya tabbatar da hakan a Dutse.
    10. An ceto fasinjoji 17 da aka yi garkuwa da su a Calabar
      Rundunar sojin ruwa ta tabbatar da cewa an ceto fasinjoji 17 da aka yi garkuwa da su a hanyar ruwa ta Calabar, bayan kwana 12 a hannun masu garkuwa da mutane. An ce an kubutar da su ba tare da biyan kudin fansa ba.