Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 13, Mayu. 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 13, Mayu. 2026

By Ahmad Habib IbrahimMayu 13, 2026No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Labaran Najeriya Na Yau – 13 Ga Mayu, 2026

1. NDC ta sanya kudin fom din shugaban kasa N60m

Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress ta fitar da jadawalin sayar da fom, tantance ’yan takara da gudanar da zabukan fidda gwani na 2027. Jam’iyyar ta sanya kudin fom din takarar shugaban kasa Naira miliyan 60.

2. Gwamna Mutfwang ya jaddada yaki da matsalar tsaro a Plateau

Caleb Mutfwang ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kokarin magance matsalolin tsaro a jihar Plateau yayin da ya karbi bakuncin daliban kwalejin soja ta Jaji.

3. Kannywood da Nollywood sun shiga jimami bayan rasuwar Alexx Ekubo

Rahotanni sun bayyana mutuwar fitaccen jarumin Nollywood, Alexx Ekubo, yana da shekaru 40 bayan fama da cutar daji (cancer) na tsawon lokaci.

4. Wike ya gana da shugaban APC na kasa

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya kai ziyara gidan shugaban APC na kasa, Nentawe Yilwatda, a Abuja yayin da ake ci gaba da rikicin siyasa a Rivers.

5. Ana sa ran Makinde zai bayyana aniyarsa ta takarar shugaban kasa

Ana sa ran gwamnan Oyo, Seyi Makinde, zai bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a wani babban taron siyasa da za a gudanar a Ibadan ranar 14 ga Mayu.

6. APC ta karbi korafe-korafe 16 daga masu neman takara a Rivers

Kwamitin daukaka kara na APC a Rivers ya karbi koke-koke daga mutane 16 da ba a tantance su ba domin shiga zaben fidda gwani na majalisar dokokin jihar.

7. Obasa zai tsaya takarar majalisar wakilai
Shugaban Majalisar Dokokin Legas, Mudashiru Obasa, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Agege Federal Constituency a Majalisar Wakilai.

8. ’Yan sanda sun kama masu garkuwa 55 a Edo

Kwamishinan ’Yan Sandan Edo ya bayyana cewa an kama mutane 55 da ake zargi da garkuwa da mutane tare da ceto mutane 58 tsakanin Maris zuwa Mayu 2026.

9. Ministan kudi ya gargadi Najeriya kan dogaro da bashi

Ministan Kudi, Taiwo Oyedele, ya ce Najeriya ba za ta ci gaba da dogaro da bashin kudi wajen ci gaba ba, yana mai kira da a samar da tsarin tattalin arziki mai dorewa.

10. Dan majalisa ya ce Peter Obi ne ya sa ya shiga NDC

Dan majalisar AMAC/Bwari, Chinedu Obika, ya ce biyayyarsa ga Peter Obi ne ya sa ya shiga jam’iyyar NDC duk da rikicin cikin gida da Labour Party ke fama da shi.

Labaran Safiyar Yau
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 30, Yuli. 2026

Yuli 30, 2026

Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN

Yuli 20, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026

Yuli 16, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 30, Yuli. 2026
  • “Idan Wani aAbu Ya Sami El-Rufai, SakamakonsaZai Zama Abin Da Ba Za A Iya Hasashe Ba” – ADC ta gargadi Tinubu
  • Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.