Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 26, Agusta. 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 26, Agusta. 2026

By Ahmad Habib IbrahimAgusta 26, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email
Demo
  1. An tarwatsa wata kungiyar “masana’antar jarirai” a Ogun
    Jami’an rundunar ‘yan sandan Ogun da ke sashen Mowe sun tarwatsa wata kungiyar da ake zargi da gudanar da haramtacciyar “masana’antar jarirai” a kauyen Abaren. An ceto mata biyu masu juna biyu da yara hudu, tare da kama mutane shida da ake zargi da hannu a harkar, ciki har da wata ma’aikaciyar jinya.
  2. Tinubu ya umarci jami’an tsaro su ceto mutanen da aka sace a Niger
    Shugaba Bola Tinubu ya umarci Rundunar Sojojin Najeriya, ‘yan sanda, DSS da sauran hukumomin tsaro da su kaddamar da wani aikin hadin gwiwa domin ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a jihar Niger. ‘Yan ta’adda sun yi awon gaba da mutane da dama daga masallatai hudu yayin sallar Juma’a a karamar hukumar Borgu.
  3. Atiku ya ce zai dawo da tallafin man fetur
    Dan takarar shugaban kasa na ADC, Atiku Abubakar, ya jaddada cewa matsayinsa kan tallafin man fetur bai sauya ba, kuma zai dawo da shi idan ya samu damar jagorantar Najeriya. Ya kuma nesanta kansa da wasu kalaman da daya daga cikin masu taimaka masa kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya yi.
  4. Dangote ya kara farashin man fetur zuwa ₦1,200 kan lita
    Matatar man Dangote ta kara farashin man fetur daga ₦1,185 zuwa ₦1,200 kan kowace lita, daga ranar 26 ga Agusta 2026. Kamfanin ya sanar da sabbin farashin man da ake dauka daga tashar rarrabawa da kuma jigilar man ta teku.
  5. An kama mutane biyu kan harbin da ya yi sanadin mutuwa a Kano
    Rundunar ‘yan sandan Kano ta tabbatar da kama mutane biyu bayan kashe mutum guda da jikkata wasu uku yayin wata liyafar aure a Tudun Yola Quarters da ke cikin birnin Kano. Wani daga cikin wadanda ake zargin ne ya bude wuta a wajen bikin.
  6. ‘Yan sanda sun ceto mutane biyu da aka yi garkuwa da su a Zamfara
    Rundunar ‘yan sandan Zamfara ta ce ta ceto mutane biyu da aka yi garkuwa da su, tare da kashe wani dan bindiga da kuma kwato bindigar AK-47 a wani samame da aka gudanar a karamar hukumar Talata Mafara.
  7. Akpabio ya ce APC na da nasarorin da za ta gabatar kafin zaben 2027
    Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce gwamnatin APC karkashin Shugaba Bola Tinubu na da nasarori da dama da za ta gabatar wa ‘yan Najeriya gabanin babban zaben 2027. Ya kuma ce gwamnatin Tinubu ta gaji mawuyacin halin tattalin arziki, inda ya yi ikirarin cewa jihohi 27 ba sa iya biyan albashi da fansho a lokacin da Tinubu ya hau mulki.
  8. APC ta musanta janye jerin kwamitin yakin neman zaben 2027
    Jam’iyyar APC ta musanta rahotannin cewa ta janye jerin sunayen kwamitin yakin neman zabenta na shugaban kasa na 2027, tana mai cewa jita-jita ce. Jam’iyyar ta ce za ta sanar da duk wani sauyi a hukumance.
  9. An daure wani dan Najeriya da ya dawo daga Canada shekara 11
    Babbar Kotun Tarayya da ke Lagos ta yanke wa Abimbola Daniel, wanda ya dawo daga Canada, hukuncin zaman gidan yari na shekaru 11 bisa laifin shigo da kilogram 2.5 na tabar wiwi da kuma mallakarsa ba bisa ka’ida ba.
  10. Shahararriyar mawakiya Dolly Parton ta rasu tana da shekara 80
    Rahotanni da dama sun bayyana cewa shahararriyar mawakiya Dolly Parton ta rasu tana da shekara 80. An ce dan uwanta, Bryan Seaver, ne ya sanar da rasuwar a shafinsa na Instagram ranar Talata. Sannan Shugaban Amurka Donald Trump ya bayar da umarnin sauke tutocin Amurka zuwa rabin sanda na tsawon mako guda domin girmama ta.

Demo
Labaran Safiyar Yau
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN

Agusta 26, 2026

Nijar ta cimma yarjejeniyar gina tashar hasken rana mai karfin megawatt 200

Agusta 26, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 18, Agusta. 2026

Agusta 18, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN
  • Nijar ta cimma yarjejeniyar gina tashar hasken rana mai karfin megawatt 200
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 26, Agusta. 2026
  • Me Ya Sa Mutum Lake Aiki Tukuru Amma Har Yanzu Yake Cikin Talauci?
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 18, Agusta. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.