Category: Labarai

  • Farashin Man Fetur na Iya Sauka a Kwanaki Kadan — Masu Rarraba Man Sun Fara Lodi daga Masana’antar Dangote

    Farashin Man Fetur na Iya Sauka a Kwanaki Kadan — Masu Rarraba Man Sun Fara Lodi daga Masana’antar Dangote

    Masu rarraba man fetur a Najeriya sun bayyana cewa farashin Premium Motor Spirit (PMS), wato man fetur, zai iya sauka a kwanaki masu zuwa bayan Masana’antar Mai ta Dangote ta sake fara lodawa ga mambobinsu.

    Shugaban Ƙungiyar Masu Rarraba Mai ta Najeriya (IPMAN)Alhaji Abubakar Maigandi, ya tabbatar wa  Jaridar DAILY POST a wata hira da aka yi da shi a ranar Litinin cewa mambobinsu sun fara lodi daga masana’antar.

    “Mambobinmu sun fara lodi daga Masana’antar Dangote a farashin ₦877 kowace lita, wanda ya tashi daga ₦820,” in ji shi.

    “Muna sa ran wannan cigaban zai kawo sauƙin karancin mai da kuma rage farashin fetur a kasuwa. Ba zan iya cewa sau nawa ne ake tsammani ba, amma akwai tabbacin ragewa.”

    Haka zalika, shugaban Ƙungiyar Masu Mallakar Tashoshin Mai (PETROAN)Billy Gillis-Harry, ya ce samuwar man a kasuwa za ta taimaka wajen rage farashi da kawo sauƙin rayuwa ga ‘yan ƙasa.

    “Idan akwai isasshen man fetur daga masana’antar Dangote ko daga manyan dillalai, ƙasar za ta cika da mai kuma hakan zai tabbatar da araha ga jama’a,” in ji shi.

    Rahotannin DAILY POST sun nuna cewa tashoshin MRSEmedebOptimaBova da wasu sun sake fara saida mai bayan ɗan tsaiko da aka samu a makonni biyu da suka gabata.

    A makonnin da suka gabata, farashin fetur ya kai tsakanin ₦940 zuwa ₦965 kowace lita a wasu sassan Abuja, lamarin da masana suka danganta da ƙarancin samarwa daga masana’antar Dangote.

    A makon da ya gabata, Mataimakin Shugaban Kamfanin Dangote IndustriesDevakumar Edwin, ya bayyana cewa an shirya lodawa sama da lita miliyan 310 na fetur daga masana’antar Dangote domin rabawa ƙasar baki ɗaya.

    Twins Empire ta ruwaito cewa kamfanonin man Najeriya ciki har da NNPCL da wasu tashoshi masu zaman kansu sun ɗaga farashin mai daga tsakanin ₦905 – ₦910 zuwa ₦940 – ₦965 kowace lita.

  • Nnamdi Kanu: Sowore da wasu sun gudu yayin da jami’an tsaro suka yi harbi da Borkonon Tsohuwa

    Nnamdi Kanu: Sowore da wasu sun gudu yayin da jami’an tsaro suka yi harbi da Borkonon Tsohuwa

    Ɗan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan Adam, Omoyele Sowore, wanda shi ne jagoran zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow, ya tsere daga wurin zanga-zangar bayan jami’an tsaro sun bude wuta da borkonon tsohuwa.

    Jami’an tsaro — da suka haɗa da ‘yan sanda da sojoji — sun mamaye wurin zanga-zangar tun da misalin ƙarfe 7:00 na safe a ranar Litinin.

    A wani faifan bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, an ga Sowore da wasu masu zanga-zanga suna gudu domin tsira da rayukansu.

    Masu zanga-zangar sun shirya ne domin tafiya zuwa fadar Aso Rock domin neman a saki Nnamdi Kanu, wanda shi ne jagoran ƙungiyar Indigenous People of Biafra (IPOB) da aka haramta.

    Sai dai Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta riga ta gargadi masu shirya zanga-zangar da kada su kuskura su gudanar da wani taro kusa da fadar shugaban ƙasa.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 16 Ga Oct, 2025

    1. Majalisar Dattawa za ta fara tantance Farfesa Joash Ojo Amupitan, SAN, a yau Alhamis, wanda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC). Daraktan bayanai na Ofishin Sakatare na Majalisar Dokoki, Bullah Audu Bi-Allah, ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa ranar Laraba.

    2. Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, ya yi murabus daga jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP). Kakakinsa, Daniel Alabrah, ne ya bayyana hakan, amma bai fayyace dalilin ficewarsa daga jam’iyyar ba.

    3. Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce gwamnoni na jam’iyyar PDP da suka koma jam’iyyar APC ya kamata su gode masa. Wike ya ce kyawawan ayyukansa ne suka ba su damar yin hakan, kuma hakan ya tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba Bola Tinubu.

    4. Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama wasu tsoffin jami’anta da aka kora, bisa zargin amfani da sunan hukumar wajen aikata zamba. Hukumar ta bayyana hakan a wata sanarwa ranar Laraba, inda ta ce waɗanda aka kama—Barry Donald da Victor Godwin—za a gurfanar da su a kotu.

    5. Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bayyana cewa canjin jam’iyya da wasu gwamnoni suka yi zuwa APC ya tabbatar da matsayar da hadakar jam’iyyun adawa suka dauka cewa ana ƙoƙarin maida Najeriya jam’iyya ɗaya. A wata sanarwa, mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Mallam Bolaji Abdullahi, ya ce jam’iyyarsu ba ta damu da abin da ya kira “rashin aminci na siyasa” daga gwamnoni ba.

    6. Sanata Seriake Dickson, wanda ke wakiltar Bayelsa ta Yamma, ya bayyana adawarsa ga yawaitar ficewar ‘yan siyasa zuwa jam’iyyar APC. Yayin da yake magana da ‘yan jarida a Majalisar Dokoki ta Ƙasa a Abuja ranar Laraba, bayan zaman majalisa, Dickson ya ce yana nan daram a PDP.

    7. Tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan ya koka da yadda aka bar manyan ayyukan da ya fara lokacin da yake Gwamnan Jihar Bayelsa, yana zargin gwamnatocin da suka biyo baya da rashin ci gaba da tsare-tsarensa na cigaba. Yayin kaddamar da otal ɗin Best Western Plus Hotel a Yenagoa ranar Laraba, Jonathan ya ce ya fara gina wasu otal-otal domin jawo zuba jari da yawon bude ido a jihar kafin ya zama mataimakin shugaban ƙasa a 2007.

    8. Babbar Kotun Jihar Kano, ƙarƙashin mai shari’a Musa Dahuru Muhammad, ta yanke wa wani kocin ƙwallon ƙafa, Hayatu Muhammad, hukuncin ɗaurin shekaru takwas a gidan yari ba tare da zabin biyan tara ba, saboda yin lalata da ƙaramin ɗan wasansa. An tabbatar da cewa wanda aka yanke wa hukuncin ya aikata laifin sau biyu a wurare daban-daban a yankin Dala.

    9. Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta ce ta ceto mutane uku da aka sace tare da kama mutane shida da ake zargi da hannu a satar, a ƙauyen Euga, ƙaramar hukumar Toro ta jihar. Mai magana da yawun rundunar, Ahmed Wakil, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa.

    10. Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya bayyana a ranar Laraba cewa ya ƙi karɓar mukamin gwamnati daga Shugaba Bola Tinubu, yana mai cewa yanzu yana son mayar da hankali kan rayuwarsa ta kashin kai bayan shekaru da dama a harkar siyasa. Fayose, wanda mamba ne na jam’iyyar PDP, ya ce duk da dangantakar sa ta kusa da Shugaba Tinubu, ba shi da niyyar shiga ko karɓar wani mukami a ƙarƙashin gwamnatin APC.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 15 Ga Oct, 2025

    1. Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, ya tafi ƙasar Birtaniya domin neman magani, kamar yadda wasu majiyoyi suka tabbatar a safiyar Talata. Rahoton ya ce ministan zai iya ci gaba da jinya a can idan likitoci suka ba da shawarar hakan.


    2. Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya, Super Eagles, ta lallasa ƙasar Benin da ci 4–0 a filin wasa na Godswill Akpabio da ke Uyo. Duk da wannan nasara, ba su samu tikitin kai tsaye zuwa gasar Copa Duniya ta 2026 ba, sai dai za su buga wasan tazarce (playoff) na ƙasashen Afirka.


    3. Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP, Kogi Central), ta bayyana cewa mata ’yan Najeriya da aka safarar zuwa Libya suna haihuwa a cikin gidajen yari. Ta bukaci hukumomin Shige da Fice da Kurkuku su hada kai da jami’an Libya domin dawo da waɗannan mata da ’ya’yansu gida Najeriya.


    4. Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa halin tattalin arziki zai inganta nan ba da jimawa ba, yana mai cewa kasar na shiga sabon mataki na ci gaban tattalin arziki. Ya bayyana haka a taron Nigeria Renewable Energy Innovation Forum (NREIF) da aka gudanar a Abuja, yana mai cewa Shugaba Bola Tinubu na jin radadin talakawa.


    5. Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dage sauraron karar da ke neman dakatar da taron gangamin jam’iyyar PDP har zuwa Alhamis, domin bangarorin biyu su sasanta rikicin lauyoyi. Alƙali Justice James Omotosho ne ya bayar da umarnin bayan rikici ya tashi tsakanin manyan lauyoyi Chris Uche (SAN) da Kamaldeen Ajibade (SAN) kan wanda ke wakiltar jam’iyyar PDP.


    6. Jam’iyyar APC ta yanke shawarar amfani da tsarin zabe na yarjejeniya (consensus) wajen zaɓen ɗan takararta na gwamna a jihar Ekiti don zaben 27 ga Oktoba. Wannan ya biyo bayan janyewar Mrs. Atinuke Omolayo, wanda ya bar Gwamna Biodun Oyebanji shi kaɗai a takara.


    7. Rundunar ’Yan Sandan Jihar Jigawa ta kama mutane 105 bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi a fadin jihar. Kakakin rundunar, SP Shi’isu Adam, ya tabbatar da hakan a lokacin da yake zantawa da ’yan jarida a Dutse ranar Talata.


    8. Majalisar Dattawa za ta tantance kuma ta tabbatar da Prof. Joash Amupitan a matsayin Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) yau Laraba, bayan wasikar da Shugaba Bola Tinubu ya aikewa majalisar ranar Talata.


    9. Majalisar Wakilai ta fara kokarin kawo karshen rikici tsakanin Gwamnatin Tarayya da kungiyar ASUU. Wannan ya biyo bayan kudirin da Sesi Oluwaseun Whingan, dan majalisa mai wakiltar Badagry, ya gabatar domin samar da mafita mai dorewa.


    10. Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya ce Gwamna Peter Mbah na Jihar Enugu yanzu shi ne jagoran jam’iyyar APC a jihar, bayan da ya koma jam’iyyar daga PDP ranar Talata. Ya bayyana hakan a lokacin taron maraba da shi a Okpara Square, Enugu.

  • Yajin Aikin ASUU Ya Tsayar Da Ayyukan Ilimi a Manyan Makarantun Najeriya

    Yajin Aikin ASUU Ya Tsayar Da Ayyukan Ilimi a Manyan Makarantun Najeriya

    Ayyukan karatu da koyarwa sun tsaya cik a yawancin jami’o’in gwamnati a fadin kasar Najeriya bayan kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) ta fara yajin aiki na makonni biyu a ranar Litinin, bayan karewar wa’adin gargadin da ta bai wa gwamnati.

    Rahoton DAILY POST ya nuna cewa jami’o’i da dama sun bi umarnin yajin aiki baki ɗaya, lamarin da ya kawo cikas ga jarrabawar da ake gudanarwa a wasu jami’o’i.

    Dalilin Yajin Aikin

    Kungiyar ASUU ta bayyana cewa ta shiga wannan yajin ne saboda gwamnatin tarayya ta kasa aiwatar da yarjejeniyar da aka kulla tun 2009 bisa tsarin Nimi Briggs Committee (2021), da kuma kin sakin albashin watanni uku da rabi na malaman da aka rike saboda yajin aikin 2022.

    Sauran bukatun sun haɗa da:

    • Sakin albashin malaman sabatical, adjunct, da part-time.
    • Biyan bashin kashi 25–35% na karin albashi na tsawon watanni 12.
    • Kammala biyan kudaden da aka cire daga albashi kamar pensioncheck-off dues, da cooperative contributions.
    • Karin kudin gyaran jami’o’in gwamnati (Revitalization Funds).

    ASUU ta kuma gargadi mambobinta cewa duk wanda bai bi umarnin yajin ba zai fuskanci hukunci mai tsanani.


    Jami’o’in da abin ya shafa

    Rahotanni sun nuna cewa jami’o’in da suka rufe ayyukan sun haɗa da:

    • Nasarawa State University, Keffi
    • Federal University, Dutse
    • University of Benin, Edo State
    • University of Nigeria, Nsukka (UNN)
    • University of Jos, Plateau State

    A wasu jami’o’in kamar Bayero University Kano (BUK) da ATBU Bauchi, an kammala jarrabawar semester kafin yajin ya fara.


    Ra’ayoyin Dalibai

    Wani dalibi a Moses Adasu University, Makurdi, mai suna Joseph Adoyi, ya ce yajin ya lalata shirinsa na karatu:

    “Ina tsammanin zan shiga mataki na uku cikin watanni uku, amma ga shi yanzu ASUU ta kawo cikas. Muna fatan wannan yajin ya ƙare cikin makonni biyu.”

    Haka kuma wata daliba ta Federal University DutseMary Ajegba, ta ce:

    “Da ba saboda yajin aikin ba, da yanzu ina yin NYSC. Sai dai na san ba za su warware wannan batun cikin makonni biyu ba. Su kan yi haka ne duk lokacin da sabon gwamnati ta hau mulki.”

    Martanin Gwamnati

    Ministan Ilimi mai taimako, Dr. Tunji Alausa, ya bayyana cewa gwamnati ta riga ta ware ₦50 biliyan don biyan Earned Academic Allowances da kuma ₦150 biliyan a kasafin kudin 2025 domin bukatun jami’o’i.

    Sai dai ASUU ta ce takardar da gwamnati ta gabatar musu “ba ta da alaka da batutuwan da aka tattauna”, musamman bangaren sharuddan aiki.

    Gwamnati kuma ta umarci Vice Chancellors su aiwatar da manufar “No Work, No Pay” ga duk malaman da suka shiga yajin aiki.

    ASUU ta ce tana shirye ta koma tattaunawa

    Shugaban ASUU, Farfesa Chris Piwuna, ya ce kungiyar tana shirye ta koma tattaunawa da gwamnatin tarayya.

    “Na samu kiran Alhaji Yayale Ahmed, shugaban tawagar gwamnati, kuma ya nuna shirin komawa tattaunawa. Haka ma Ministar Kwadago ta kira ni. ASUU tana nan a shirye don magance matsalar ta hanyar tattaunawa.”


     Tasirin Yajin Aiki

    • Jarrabawa sun tsaya a jami’o’i da dama.
    • Dalibai da dama sun fara barin harabar jami’o’i.
    • Harsashen karatun wasu ya lalace saboda tsayawar karatu.

    Yajin aikin ASUU ya sake dawo da rudani a fannin ilimi a Najeriya, yayin da malaman jami’o’i ke bukatar gwamnati ta cika alkawuranta. Duk da shirin komawa tattaunawa, yanzu haka ɗalibai da malamai na cikin rashin tabbas game da makomar karatun su.

  • Makomar Peter Obi a jam’iyyun ADC da LP na cikin rudani : 2027

    Makomar Peter Obi a jam’iyyun ADC da LP na cikin rudani : 2027

    Tsohon Gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, na fuskantar rashin tabbas kan dandalin siyasa da zai tsaya a zaben shugaban kasa na 2027, yayin da ake samun rudani a cikin jam’iyyun da yake da alaka da su.

    Rahoton DAILY POST ya nuna cewa Obi, wanda ya tsaya takarar shugaban kasa a 2023 karkashin jam’iyyar Labour Party (LP), na daga cikin manyan jiga-jigan ‘yan adawa da ke shirin haduwa domin hambarar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben gaba.

    A ranar 2 ga Yuli, 2025, shugabannin adawa da suka hada da Obi, tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, tsohon Shugaban Majalisar Dattawa David Mark, tsofaffin gwamnonin Kaduna da Ribas, Nasir El-Rufai da Rotimi Amaechi, sun amince da jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a matsayin dandalin da za su tsaya takara a 2027.

    Sai dai, burin Obi na samun tikitin ADC yana raguwa sosai, domin manyan jam’iyyar sun fi karkata zuwa ga Atiku.

    Wani tushe daga cikin jam’iyyar ya shaida wa DAILY POST cewa ba za a samu dan takarar hadin kai ba, inda ya ce ADC za ta gudanar da zaben fidda gwani (primary election) kamar yadda sauran jam’iyyu ke yi.

    A bangaren Obi kuwa, rahotanni sun bayyana cewa baya da niyyar fuskantar Atiku a cikin zaben fidda gwani.

    “Ba za mu shiga zaben da aka ‘dollarize’ ba” – Kungiyar Obidient

    Kungiyar goyon bayan Obi wato Obidient Movement ta ce shugaban su ba zai shiga kowace irin zabe ta delegates da ake amfani da kudi ba.

    Dr. Yunusa Tanko, Koodinetan kasa na kungiyar, ya bayyana cewa siyasar Obi ba ta karɓi tsarin “zaben da ake biyan delegates da daloli” ba.

    A cewarsa:

    “Peter Obi ba zai shiga zaben delegates da ake biya da kudi ba.

    Wadannan mutane da suka tara dukiya mai yawa za su iya cin zarafinsa.

    Mu muna tafiya da tsarin siyasa daban. Obi ba zai shiga zaben da aka cika da kudi ba.”

    Yunusa ya kuma ce tun da shugabancin kasa an ware shi ga kudu, bai kamata a cigaba da maganar dan takarar Arewa ba.

    A gefe guda, Atiku ya bayyana cewa ba zai ja da baya don kowa a jam’iyyar ADC ba.

    Da aka tambayi ko Obi zai iya sauya sheka zuwa wata jam’iyya, Tanko ya ce:

    “Idan muka kai ga wannan matakin, sai mu dauki mataki.”

    ADC ta ki yin tsokaci kan batun zaben fidda gwani

    Mai magana da yawun jam’iyyar ADC na kasa, Bolaji Abdullahi, ya ce jam’iyyar bata fara tattaunawa kan wanda zai tsaya mata a zaben 2027 ba.

    Ya ce:

    “Babu wanda ke tattaunawa yanzu kan dan takarar hadin kai ko zaben fidda gwani.

    A yanzu mu na kan kokarin gina jam’iyyarmu, ba tattaunawa kan dan takarar shugaban kasa ba.”

    Game da dalilin da yasa Obi bai yi rajista da jam’iyyar ba, Bolaji ya ce:

    “Obi da El-Rufai ba su zama mambobi na ADC ba tukuna.

    Obi yana son ya tallafa wa ‘yan takarar jam’iyyarsa ta asali kafin ya shiga ADC gaba ɗaya bayan zaben Anambra.”

    Lalacewar LP na iya hana Obi tsayawa takara

    Wasu masu sharhi sun bayyana cewa Obi ba zai iya amfani da jam’iyyar Labour Party (LP) a 2027 ba saboda rikicin cikin gida da ke damun jam’iyyar.

    Masanin siyasa Dr. Anabi Samuel, ya ce rikicin da ke tsakanin Julius Abure da wasu mambobi zai iya hana Obi samun tikitin jam’iyyar.

    A cewarsa:

    “Peter Obi ya samu abokan gaba a LP.

    Ko da ya samu tikiti, wadannan mutanen da ke cikin jam’iyyar za su iya hana shi cin nasara.”

    Ya kuma kara da cewa idan Obi bai samu tikitin ADC ba, zai fi kyau ya jinkirta burinsa, sai dai idan PDP ta amince ta bashi tikiti.

    LP: Ba za mu bawa Obi tikitin kai tsaye ba

    Duk da cewa wasu suna ganin Obi ne ya daukaka LP a siyasar Najeriya, jam’iyyar ta bayyana cewa ba za ta bashi tikitin kai tsaye (automatic ticket) ba.

    Mai magana da yawun LP na kasa, Obiora Ifoh, ya ce:

    “Zaben fidda gwani zai kasance cikin dimokuradiyya.

    Duka mukamai za a bude su domin masu sha’awa su tsaya.

    Bai kamata a bawa kowa tikitin kai tsaye ba.”

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 09, Oct. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 09 Ga Oct, 2025

    1. Bankin Duniya ya ce Najeriya ta tabbatar da sauyin tattalin arziki ya amfani talakawaBankin Duniya (World Bank) ya bukaci Najeriya da ta tabbatar da cewa sakamakon gyare-gyaren tattalin arziki da ake yi ya zama abin amfani ga jama’a. Shugaban Bankin Duniya a Najeriya, Mathew Verghis, ya bayyana cewa sama da mutane miliyan 139 na rayuwa cikin talauci a kasar, don haka gwamnati ta mayar da hankali wajen sauƙaƙa rayuwar jama’a.

    1. Sojoji sun ceto mutum 37 da aka yi garkuwa da suRundunar sojin Najeriya ta sanar da cewa dakarunta sun ceto mutum 37 da aka yi garkuwa da su a yayin wani babban farmaki kan ‘yan ta’adda. An kashe ‘yan ta’adda 9, an kama mutane 8, tare da kwace makamai da dama a cikin wannan samame.

    1. Naira ta kara karfi a kasuwaNaira ta karu zuwa ₦1,490/$1 a kasuwar bayan fage, daga ₦1,495/$1 a jiya. Haka kuma a kasuwar musayar kudade ta gwamnati (NFEM), Naira ta karu zuwa ₦1,469/$1, bisa rahoton tattalin arziki na yau Laraba.

    1. Akpabio da Abba Moro sun yi takaddama a Majalisar DattawaShugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, da Jagoran ‘Yan adawa, Sanata Abba Moro, sun yi gardama kan yawaitar sauya sheka daga jam’iyyun adawa zuwa APC. Akpabio ya ce rashin tsari a jam’iyyun adawa ne ke sa hakan, sai dai Moro ya mayar da martani cewa adawa za ta ci gaba da tsayawa da kafafunta komai rashi.

    1. Orji Kalu ya ce Tinubu zai sake lashe zabe a 2027Tsohon Gwamnan Abia, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai sake lashe zaben 2027, yana mai cewa babu wanda zai iya kayar da shi – ko Atiku AbubakarGoodluck Jonathan, ko Peter Obi.

    1. ’Yan sanda sun dakatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhuRundunar ’yan sanda ta dakatar da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (tinted glass permit) bayan an ba ta sammaci daga kotu. Mai magana da yawun rundunar FCT, Josephine Adeh, ce ta tabbatar da hakan a wani shirin talabijin.

    1. INTERPOL ta tabbatar da kama dan Najeriya da ya yi damfara ta soyayyaHukumar INTERPOL ta tabbatar da cewa jami’an tsaro a Argentina sun kama wani dan Najeriya mai suna Ikechukwu N., wanda ake zargi da shirya damfara ta yanar gizo ta hanyar soyayya wadda ta shafi mata dubban a kasashe daban-daban.

    1. Wike ya gargadi shugaban AMAC kan sa suna kan tituna ba bisa ka’ida baMinistan FCT, Nyesom Wike, ya gargadi shugaban karamar hukumar AMACChristopher Maikalangu, da ya daina sanya sunaye a tituna da hanyoyi da ba tare da izini daga ma’aikatar babban birnin tarayya ba.

    1. Kotu ta jinkirta sauraron karar EFCC har zuwa Oktoba 9Wata kotu ta musamman a Ikeja ta dage shari’ar EFCC har zuwa ranar 9 ga Oktoba, domin ta yanke hukunci kan sahihancin hujjojin dijital da hukumar ta gabatar. Alkalin kotun, Justice Rahman Oshodi, ya ce ya bukaci karin lokaci don nazarin shaidun da aka gabatar.

    1. Kotu ta kara mako guda ga kwamitin likitoci don duba lafiyar Nnamdi KanuKotun Tarayya a Abuja ta bai wa kwamitin likitocin da ke duba lafiyar jagoran IPOBNnamdi Kanu, karin mako guda, bayan sun kasa kammala binciken lafiyarsa cikin kwanaki takwas da kotu ta diba a baya.