Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Tsohon Ministan Kimiyya, Uche Nnaji ya musanta zargin ƙirƙirar takardun shaidar karatu

Tsohon Ministan Kimiyya, Uche Nnaji ya musanta zargin ƙirƙirar takardun shaidar karatu

By Ahmad Habib IbrahimYuli 13, 2026No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email
Demo

Tsohon Ministan Ƙirƙire-ƙirƙire, Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji, ya musanta zargin da ake masa na ƙirƙirar takardar shaidar digirinsa da kuma takardar kammala aikin bautar ƙasa (NYSC) bayan gwamnatin tarayya ta gurfanar da shi a kotu.

Hukumar ICPC (Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission) ce ta shigar da ƙarar, kuma an gurfanar da shi a gaban Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

Demo

Ana tuhumar Nnaji da laifuffuka guda shida, ciki har da zargin ƙirƙirar takardar digiri daga Jami’ar Najeriya da ke Nsukka (UNN) da kuma takardar kammala bautar ƙasa ta NYSC, waɗanda ya gabatar yayin tantance shi a matsayin minista a shekarar 2023.

Har ila yau, ana zarginsa da karɓar kusan Naira miliyan 29.5 a matsayin albashi da wasu alawus-alawus ta hanyar yaudara, tare da zargin safarar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba.

Bayan ya musanta dukkan tuhume-tuhumen a ranar Litinin, lauyan gwamnati ya sanar da kotu cewa ya shirya fara shari’ar, inda ya bayyana cewa shaidu uku sun riga sun hallara a kotun.

Sai dai lauyan Nnaji, Ogwu Onoja (SAN), ya nemi ƙarin lokaci domin shirya kare wanda yake wakilta, tare da sanar da kotu cewa sun riga sun shigar da buƙatar beli tun ranar 9 ga Yuli.

Lauyan gwamnati bai yi adawa da neman belin ba.

A hukuncin da ta yanke, Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta ba Nnaji beli kan kuɗin Naira miliyan 20, tare da sharadin gabatar da mutum ɗaya da zai tsaya masa, wanda dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai matsayi ba ƙasa da Level 15, kuma mazaunin Abuja.

Kotun ta kuma umarce shi da ya miƙa fasfo ɗinsa na aiki da na kansa har zuwa lokacin da za a kammala shari’ar.

Rahotanni sun ce gurfanar da Nnaji ya biyo bayan watanni na bincike kan sahihancin takardunsa, inda aka ruwaito cewa Jami’ar UNN da Hukumar NYSC sun musanta sahihancin takardun da ake magana a kansu.

An kama Nnaji ne a ranar 30 ga Yuni, 2026, a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, lokacin da jami’an DSS suka tsare shi bayan ya dawo daga Enugu.

An ce an kama shi ne bisa umarnin kotu da aka bayar tun ranar 11 ga Yuni, 2026, bayan ya kasa amsa gayyata da dama domin amsa tambayoyi a binciken da ake yi.

Nnaji ya yi murabus daga mukaminsa na minista a ranar 7 ga Oktoba, 2025, inda ya bayyana cewa ya yi hakan ne domin mutunta tsarin shari’a, yayin da ya ci gaba da musanta aikata wani laifi, yana mai cewa akwai siyasa a bayan shari’ar.

A halin yanzu, Uche Nnaji shi ne ɗan takarar gwamnan jihar Enugu na jam’iyyar PDP.

Demo
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Sarkin Gumel Alhaji Dr. Ahmed Muhammad Sani II, CON Ya Rasu A Yau 3 Ga Nuwamba 2026

Satumba 3, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 2, Nuwamba 2026

Satumba 2, 2026

Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN

Agusta 26, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Sarkin Gumel Alhaji Dr. Ahmed Muhammad Sani II, CON Ya Rasu A Yau 3 Ga Nuwamba 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 2, Nuwamba 2026
  • Gwamnatin Ghana ta ƙi karɓar tallafin cedi miliyan 20 daga MTN
  • Nijar ta cimma yarjejeniyar gina tashar hasken rana mai karfin megawatt 200
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 26, Agusta. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.