Sojin Najeriya sun daƙile harin ƴan bindiga a jihar Kano

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta JTF sun samu nasarar daƙile wani hari da ƴan bindiga suka tsara kai wa wasu garuruwa a ƙaramar hukumar Shanono da ke jihar Kano da ke arewacin Najeriya, bayan musayar wuta da aka shafe tsawon lokaci ana yi.

Musayar wutar wadda aka fara tun cikin daren alhamis har zuwa wayewar safiyar juma’ar nan, ta afku ne a Yankwada da Babanduhu da sauran ƙauyuka da ke maƙotaka da yankin.

Da yake tabbatar da lamarin ga kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN, mai magana da yawun rundunar a Kano, Major Zubair Babatunde, ya ce ƴan bindigar sun tsara kutsawa cikin ƙauyukan ne a kan babura tare da harbi kan mai uwa da wabi.

Babatunde ya ce harin na a matsayin na ramuwa, biyo bayan hare-haren da rundunar ta kai wa ƴan bindigar, lamarin da ya kai ga mutuwar da dama daga cikinsu a makon da ya gabata.

Babatunde ya ƙara da cewa, daƙile harin da suka samu nasarar yi ya sanya ba a samu asarar rayukan ko da mutum guda ba, ko rasa dukiya a waɗannan yankuna da abun ya shafa.

Shi ma, shugaban kwamitin dake kula da tsaron yankin Shanono da Bagwai ya ce maharan sun zo ɗaukar fansa ne sakamakon rasa mambobinsu 9 da su ka yi a musayar wuta tsakaninsu da dakarun Najeriya.

Dakarun rundunar JTF ƙarƙashin Operation MESA da birgediya na 3 a rundunar tsaron Najeriya yake jagoranta, sun yi nasarar halaka ƴan bindiga aƙalla 19 a ƙaramar hukumar ta Shanono yayin arangamar da su ka yi a watan Oktoban shekarar 2025.