Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Eid-ul-Mawlid: Gwamnatin Tinubu ta ayyana hutun ranar Juma’a

Eid-ul-Mawlid: Gwamnatin Tinubu ta ayyana hutun ranar Juma’a

By Ahmad Habib IbrahimSatumba 3, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Gwamnatin Tarayya karkashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu ta ayyana ranar Juma’a, 5 ga Satumba, 2025, a matsayin hutun gwamnati domin bikin tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

A wata sanarwa da Sakataran Dindindin na Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Dr Magdalene Ajani ta fitar a ranar Talata, Ministan Harkokin Cikin Gida, Dr Olubunmi Tunji-Ojo, ya yi wannan sanarwa a madadin gwamnatin tarayya.

Ministan ya mika gaisuwar fatan alheri ga musulmai a Najeriya da ma duniya baki ɗaya, yana mai kira ga al’ummar Musulmi da su yi koyi da dabi’un Annabi Muhammad (SAW) na zaman lafiya, soyayya, tawali’u, hakuri da tausayawa. Ya ce waɗannan halaye na da matuƙar muhimmanci wajen gina ƙasa mai haɗin kai da cigaba.

Haka kuma, ya yi kira ga ‘yan Najeriya na dukkan addinai da su yi amfani da wannan lokaci wajen yi wa ƙasa addu’a domin zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali, tare da goyon bayan ƙoƙarin gwamnati na samar da daidaito da ci gaban dorewa.

“Bikin Eid-ul-Mawlid yana bamu wata dama ta ƙarfafa zumunci, inganta zaman lafiya a tsakanin al’umma, da kuma koyon darussan Annabi na mutunta juna da sadaukar da kai don jin ƙai,” in ji Tunji-Ojo.

Ya ƙara da jan hankalin ‘yan ƙasa da su kasance masu bin doka, masu lura da tsaro, tare da tallafa wa manufofin gwamnati da nufin inganta walwalar kowa. Ya kuma yi fatan Musulmi za su yi biki cikin farin ciki da kwanciyar hankali.

Maulud Mouloud
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN

Yuli 20, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026

Yuli 16, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026

Yuli 15, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Dangote: Najeriya na iya fara sayen fetur da dizal da dalar Amurka – PETROAN
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 16, Yuli. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 15, Yuli. 2026
  • Tsohon Ministan Kimiyya, Uche Nnaji ya musanta zargin ƙirƙirar takardun shaidar karatu
  • Gwamnatin Tarayya ta dakatar da ƙarin kuɗin jarabawar WAEC da NECO bayan suka
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.