Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 4, Aug. 2025

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 4, Aug. 2025

By Ahmad Habib IbrahimAgusta 4, 2025No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

1. El-Rufai Ya Gargadi Tinubu da APC:
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi gargadin cewa za a lalata hadin kan al’umma gaba ɗaya idan Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC suka sake komawa mulki a 2027. Ya bayyana haka ne a Sokoto yayin gangamin jam’iyyar adawa ADC.

2. D’Tigress Sun Yi Tarihi:
Kungiyar kwallon kwando ta mata ta Najeriya, D’Tigress, sun zama ƙungiyar farko da ta ci kofin FIBA AfroBasket sau biyar a jere bayan doke Mali. Sun samu gurbin kai tsaye zuwa gasar cin kofin duniya ta 2026 a Berlin, Jamus.

3. Peter Obi Ya Ƙara Jaddada Wa’adin Shekara 4:
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a 2023, Peter Obi, ya sake bayyana aniyarsa ta yin wa’adi guda na shekaru hudu idan aka zaɓe shi a 2027. Wannan martani ne ga suka daga Gwamnan Anambra, Chukwuma Soludo.

4. Gini Ya Rufta Kan Mai Hotel:
Wani gini na hotel da ake ginawa a Uromi, Jihar Edo, ya rufta ya kashe mai shi, Andrew Isesere. Ma’aikata sama da 20 sun sha da kyar, wasu kuma sun ji rauni.

5. LASU Ta Dakatar da Jarabawa:
A Jami’ar Jihar Legas (LASU), majalisar jami’ar ta dakatar da dukkan harkokin karatu da al’amuran jami’a, ciki har da jarabawar zangon biyu na shekarar 2024/2025, saboda yajin aikin malaman jami’ar.

6. SDP Ta Maka INEC a Kotu:
Jam’iyyar SDP ta shigar da ƙara kan hukumar zaɓe (INEC) saboda ƙin amincewa da ’yan takararta a zaɓukan cike-gurbi a jihohi 12.

7. ’Dan Limamin Abuja Ya Rasa Ransa:
Attahiru Abubakar, ɗan Chief Imam na Kuchibuyi a Abuja, ya mutu bayan harbin ’yan sanda a rikicin fili, yayin da yayansa Abass ya samu rauni mai tsanani.

8. An Kama Mutanen Benin 10:
Rundunar ’yan sandan Ondo ta cafke ’yan asalin Jamhuriyar Benin 10 da ake zargi da hannu a safarar mutane a jihar.

9. Hasashen Ruwa da Ƙarfin Iska:
Hukumar NiMet ta sanar da yiwuwar ruwan sama mai ƙarfi da guguwa daga Litinin zuwa Laraba, tare da yiwuwar ambaliyar gaggawa a wasu yankuna.

10. PDP Ta Fitar da Jadawalin Zaben Shugabanni:
Jam’iyyar PDP ta sanar da jadawalin babban taron zaben shugabanninta, wanda za a yi a ranar 15-16 ga Nuwamba. Siyar da fom za ta fara 3 ga Satumba zuwa 22 ga Satumba, sannan mayar da fom zai kasance kafin 26 ga Satumba.

Labaran Safiyar Yau
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Juma’a 5, Yuni, 2026

Yuni 5, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 4, Yuni. 2026

Yuni 4, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 3, Yuni. 2026

Yuni 3, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Juma’a 5, Yuni, 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 4, Yuni. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 3, Yuni. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 2, Yuni. 2026
  • Role Din Adam Zango Ne Aka Bawa Jarumin – Ahmad Editer
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.