Tag: Labaran Safiyar Yau

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 26, Aug. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 26 Ga Agusta, 2025

    PDP ta zabi kudu a matsayin yankin da zai fitar da dan takarar shugaban kasa
    Kwamitin Zartaswa na Kasa (NEC) na jam’iyyar PDP ya amince da kudirin kwamitin rabon mukamai na kasa da ya ce kudu ce za ta fitar da dan takarar shugaban kasa a zaben 2027.

    ACF ta gargadi kan halin da Arewa ke ciki
    Kungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ta ce Arewa tana fuskantar matsanancin tsaro, talauci da matsalar muhalli, tana mai gargadi cewa ba za ta kara yin shiru ba a irin wannan hali.

    PDP ta tabbatar da Umar Damagum a matsayin shugaban jam’iyya na dindindin
    Kwamitin NEC na PDP ya tabbatar da Umar Damagum a matsayin shugaban jam’iyya na kasa. A jawabin sa ya gode wa sauran shugabanni bisa goyon bayan da suka bashi.

    Hadarin mota ya kashe mutane hudu a Delta
    Mutane hudu sun mutu yayin da manyan motar daukar siminti ta kife a kan babur mai kafa uku a kusa da gadar Niger ta biyu, Asaba. Hukumar FRSC ta ce gudu fiye da kima ce ta haddasa hatsarin.

    NDLEA ta kama babban dillalin miyagun kwayoyi a Kano
    Hukumar NDLEA ta cafke Mohammed Abubakar, wanda aka fi sani da Bello Karama, da wasu mutane biyar da ake zargi da dasa miyagun kwayoyi cikin jakunkunan fasinjoji a filin jirgin Kano.

    Naira ta karu a kasuwar bayan fage
    Naira ta karu zuwa ₦1,540/$1 a kasuwar bayan fage daga ₦1,550/$1 a karshen mako, amma a kasuwar FX ta fadi zuwa ₦1,536.99/$1.

    Gwamnati ta rufe makarantun koyar da malamai 22 marasa lasisi
    Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta gano ta kuma rufe haramun makarantun koyar da malamai 22 a fadin Najeriya.

    Hadarin kwale-kwale ya kashe manoma uku a Borno
    Kwale-kwale dauke da manoma 20 ta kife a kogin Kubo, Jihar Borno, sakamakon lodi fiye da kima. Mutane 17 aka ceci, uku sun rasu.

    INEC ta ce sama da mutane miliyan 1.3 sun yi rajistar zabe a mako guda
    Hukumar INEC ta ce mutane 1,379,342 sun kammala rajista ta yanar gizo cikin mako guda na fara aikin ci gaba da rajistar masu kada kuri’a.

    Gwamnati ta kaddamar da sabon shafin yanar gizo don rijistar malamai
    Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da dandalin yanar gizo domin samar da bayanan malamai na gaskiya da kuma tabbatar da bin ka’idoji a fannin ilimi.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau litinin 25, Aug. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 25 Ga Agusta, 2025

    1. Sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Benue

    Majalisar Dokokin Jihar Benue ta zaɓi Hon. Berg Afled Emberga, ɗan majalisa mai wakiltar Makurdi North, a matsayin sabon Kakaki. Emberga ya maye gurbin Hon. Aondona Dajoh wanda ya yi murabus bayan rikicin shugabanci da ya daɗe a majalisar.

    2. Sojoji sun lalata matatun mai na bogi a Niger Delta

    Rundunar Sojoji ta 6 Division ta lalata matatun mai na bogi guda 9, ta kwace lita 32,000 na man da aka sace, tare da kama mutane 69 da ake zargi da fasa ƙwauri.

    3. Mutum 6 sun rasu a hatsarin jirgin ruwa a Sokoto

    Aƙalla mutane 6 sun mutu, 3 sun ɓace a hatsarin jirgin ruwa a Garin Faji, Sabon Birni, Sokoto, yayin da mazauna yankin ke gudu daga farmakin ’yan bindiga.

    4. Sojojin Najeriya sun hallaka ’yan ta’adda 30 a Borno

    Dakarun Operation Hadin Kai sun bomba fiye da ’yan ta’adda 30 da suka yi yunkurin shiga Najeriya daga iyakar Kamaru a kusa da Kumshe, Borno.

    5. Falana ya bukaci a mika N32.7bn ga NSIPA

    SAN Femi Falana ya bukaci hukumar EFCC ta mika N32.7 biliyan da $445,000 da ta kwato daga jami’an Ma’aikatar Harkokin Jinƙai zuwa National Social Investment Programme Agency (NSIPA) domin amfanin jama’a.

    6. NiMet: Za a yi ruwan sama da ƙanƙara daga Litinin zuwa Laraba

    Hukumar NiMet ta yi hasashen ruwan sama da guguwar ƙanƙara a jihohin Arewa da dama ciki har da Jigawa, Zamfara, Kano, Kaduna, Bauchi, Yobe da Katsina daga Litinin.

    7. Farashin fetur ya ƙaru zuwa N823/lita

    Manyan kamfanonin rarraba mai – Dangote Refinery, Aiteo da AA Rano – sun ƙara farashin fetur a matakin N823/lita, bayan hauhawar farashin man duniya daga $65 zuwa $67 kowace ganga.

    8. ADC ta bukaci a ayyana dokar ta-baci a Katsina da Zamfara

    Jam’iyyar ADC ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya ayyana dokar ta-baci a Katsina da Zamfara sakamakon hare-haren da suka kashe mutane fiye da 140 cikin watanni biyu.

    9. Ƴan sanda sun kama fitaccen mai garkuwa da mutane a Nasarawa

    Rundunar ’Yan sanda a Nasarawa ta kama wani shahararren mai garkuwa da mutane, Mohammed Bammi (Zomo) na kauyen Yelwa, bisa bayanan leƙen asiri.

    10. ’Yan sanda sun damke dillalan miyagun ƙwayoyi a Uyo

    Rundunar ’Yan sanda a Akwa Ibom ta kama mutane 4 da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a Uyo, bayan samamen da aka kai a wuraren sayar da miyagun ƙwayoyi.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Jumaʼa 22, Aug. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 22 Ga Agusta, 2025

    1. Rikicin Zoning PDP:
    Wasu shugabannin PDP na jihohi daga Kudancin Najeriya, da wasu ‘yan majalisa da tsoffin mambobin NWC sun nesanta kansu daga taron Zoning da ake yi a Legas. Taron na Legas zai yanke hukunci kan matsayar Kudancin PDP wajen rabon mukamai.

    2. Harin Plateau:
    Aƙalla manoma 15 aka kashe a sabuwar hari a ƙauyuka bakwai na Chakfem LGA, Mangu, Plateau. Masu harin sun ƙone gidaje da sace dabbobi.

    3. Harin Kaduna:
    ‘Yan bindiga sun kai hari Kakangi, Birnin Gwari (Kaduna), inda suka kashe manoma 5 – 4 daga cikin su dangi guda ɗaya ne.

    4. Maganar ACF:
    Kungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ta nuna damuwa kan yadda matsalolin ‘yan bindiga da ta’addanci ke ƙara jefa Arewa cikin bala’i, tare da jawo rayuka da dukiyoyi su na salwanta.

    5. Cutar Abortion a Akwa Ibom:
    ‘Yan sanda sun kama wani Sunday Okon Akpan, wanda ya yi ikirarin likita ne, bisa zargin kashe mace mai shekaru 35 yayin gwada yi mata ciki zubarwa a asibitinsa na bogi.

    6. Maganar Makinde:
    Gwamna Seyi Makinde na Oyo ya ce PDP ba za ta sauka matakin “taba-kashe” irin na Ministan Abuja, Nyesom Wike ba. Ya ce NEC na PDP za ta yanke hukunci kan zoning a taronta ranar Litinin mai zuwa.

    7. Ziyarar Shugaba Tinubu:
    Shugaba Bola Tinubu ya baro Japan, ya nufi Brazil don ziyara ta ƙasa, inda zai isa ranar Lahadi, 24 ga watan Agusta. Ya tsaya a Los Angeles kafin tafiya Brasília.

    8. Jungle Justice a Kwara:
    ‘Yan sanda a Ilorin sun la’anci yadda jama’a suka yi wa wata mata talaka duka har aka raunata ta, bisa zargin ɓatacciyar ƙarya cewa mai garkuwa da mutane ce, a kasuwar Ipata.

    9. Janar Musa kan Zaben 2027:
    CDS, Janar Christopher Musa, ya danganta yawaitar kashe-kashe a ƙasar nan da shirin zaben 2027, yana mai cewa ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga sun ƙara tasiri a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma.

    10. Tattalin Arziki – Ajiyar Kudi:
    Babban Bankin Najeriya ya bayyana cewa kudin ajiya na ƙasar sun kai dala $41bn a ranar 19 ga Agusta 2025 – mafi girma cikin shekaru 44 watanni, tun daga Disamba 2021.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 20, Aug. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 20 Ga Agusta, 2025

    1. Harin Katsina – Akalla mutum 13 suka mutu, da dama kuma sun jikkata a harin da aka kai wa al’ummar Unguwar Mantau, Malumfashi, Katsina, a lokacin da suke sallar Asuba.

    2. Tsaro a jirgin sama – Hukumar NCAA ta umarci cewa dukkan wayoyi da na’urorin lantarki a kashe su yayin matakan da suka fi muhimmanci a tafiyar jirgin.

    3. Shari’ar harin Owo – DSS ta roki kotun tarayya da ke Abuja kada ta ba da belin mutum biyar da ake tuhuma da harin Cocin Katolika na Owo a 2022, saboda alaƙarsu da ƙungiyoyin ta’addanci na ƙasashen waje.

    4. Fadar siyasa – Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce burin Rotimi Amaechi na neman shugabancin ƙasa a 2027 ya mutu tun kafin ya fara, ya kuma soki Babachir Lawal kan rashin zama mataimakin shugaban kasa.

    5. Zargin cin hanci a NNPC – Kotun tarayya a Abuja ta bayar da umarnin rufe asusun Jaiz Bank guda hudu da aka danganta da tsohon GMD na NNPCL, Mele Kyari, bisa tuhumar rashawa.

    6. Binciken Hajj 2025 – EFCC ta yi wa manyan jami’an NAHCON tambayoyi kan zargin almundahana a aikin Hajjin bana, ciki har da Aliu Abdulrazak da Aminu Muhammed.

    7. Tattalin arziki – Naira ta fadi zuwa ₦1,555/$1 a kasuwar bayan fage, amma ta karu zuwa ₦1,534.5/$1 a kasuwar canjin kudade ta NFEM.

    8. ADC da manyan ‘yan siyasa – Jam’iyyar ADC ta ce manyan ‘yan siyasa kamar Atiku Abubakar, Peter Obi, da Rotimi Amaechi za su ci gaba da zama tsintsiya madaurinki guda domin sauya Najeriya.

    9. Sauya sheka – Wasu mambobin PDP a Ayedire, Osun, sun koma jam’iyyar ADC karkashin jagorancin Tunji Ogunrinu, inda jami’an Omoluabi Progressives suka tarbe su.

    10. Zaben Zamfara – INEC ta sanya Alhamis 21 ga Agusta a matsayin ranar yin zaben ƙarin kujeru a Kaura-Namoda South, bayan da aka ce sakamakon zaben makon jiya ya kasance ba a kammala ba.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 18, Aug. 2025

    Takaitattun Labaran Safiyar Yau Litinin 18, Aug. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 18 ga Agusta, 2025

    1. Akalla ’yan kasuwa 30, ciki har da mata, ake zargin sun rasu a wani hatsarin kwale-kwale da ya auku a ranar Lahadi a kauyen Kojiyo, karamar hukumar Goronyo, jihar Sokoto. Rahotanni sun bayyana cewa mutanen na kan hanyarsu ta zuwa kasuwar mako-mako ta Goronyo ne lokacin da kwale-kwalen da ke ɗauke da fasinjoji da kaya ya kife misalin ƙarfe 1:30 na rana.

    2. Sarkin Zuru na jihar Kebbi, Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya), wanda aka fi sani da Gomo II, ya rasu yana da shekara 81. Marigayin ya rasu a asibiti a birnin Landan a ranar Asabar bayan gajeriyar rashin lafiya. Ya bar mata huɗu da ’ya’ya bakwai.

    3. Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) reshen Kano ta yi watsi da sakamakon zaɓen sake yin kuri’a na majalisar dokoki a mazabar Ghari/Tsanyawa, tana zargin an tafka magudi da kuma haɗin baki tsakanin ’yan siyasa da jami’an hukumar INEC. Shugaban jam’iyyar na jihar, Comrade Hashimu Sulaiman Dungurawa, ya ce INEC ta hana ’yan ƙasa damar zaɓensu, bayan ta ayyana ɗan takarar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

    4. Hukumar NDLEA ta cafke shahararren dillalin miyagun ƙwayoyi, Sunday Ibigide, a Asaba, jihar Delta, bayan farautar da ta ɗauki tsawon shekaru uku. An kama shi tare da mataimakinsa Clement Osuya (27) yayin da suke ƙoƙarin jigilar tulin tabar wiwi guda 250 masu nauyin kilo 138 a cikin motar rarraba kaya. Kakakin NDLEA, Femi Babafemi, ya ce Ibigide yana ta gudun hijira tun watan Maris 2022 bayan kama kilo 24.1 na wiwi da gram 10 na “molly” da aka danganta masa.

    5. Rundunar ’yan sandan jihar Edo ta sanar da cafke wani ɗan sanda tare da wasu fararen hula uku bisa zargin yin fashi da makami da kuma cuwa-cuwa a birnin Benin. An bayyana waɗanda ake zargin da Inspector Ojo Oloruntobi, Charles Onah, Joseph Ohis, da Enoma Agho. Rahotanni sun ce su ne ke da alhakin jerin fashi da cuwa-cuwa da cin zarafin jama’a a cikin garin.

    6. Hukumar INEC ta bayyana zaɓen kujerar majalisar jihar Zamfara a mazabar Kaura-Namoda South a matsayin wanda bai kammala ba, saboda matsaloli a rumfunan zaɓe guda biyar. Jami’in tattara sakamakon, Farfesa Lawal Sa’adu, ya bayyana hakan da misalin ƙarfe 1:30 na safe, inda ya ce matsalolin a unguwannin Sakajiki da Kyambarawa ne suka tilasta wannan mataki.

    7. Jam’iyyar APC ta gode wa ’yan Najeriya bisa irin goyon bayan da suka nuna mata wanda ya kai ga samun nasarori a zaɓen cike guraben ’yan majalisa da aka gudanar a jihohi 12 na ƙasar. Kakakin jam’iyyar na ƙasa, Mista Felix Morka, a cikin wata sanarwa a Abuja ranar Lahadi, ya danganta wannan nasara da amincewar jama’a ga jagorancin Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu.

    8. Jam’iyyar APC ta yi watsi da sakamakon zaɓen kujerar majalisar dattawan Anambra ta Kudu da aka gudanar ranar Asabar. INEC ta bayyana Dr Emmanuel Nwachukwu na jam’iyyar APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen da ƙuri’u 90,408. Shugaban APC na jihar Anambra, Chief Basil Ejidike, ya zargi cewa an tsare ɗan takararsu a gidansa ta hannun jami’an tsaron Anambra Vigilance Group.

    9. An ruwaito cewa wasu ’yan Najeriya biyu da aka fi sani da Collins da Osas sun mutu a Tripoli, babban birnin Libiya, cikin yanayi da ake kyautata zaton yana da alaƙa da guba. An tattaro cewa mutanen biyu, waɗanda ke zama a Misrata, sun yi tafiya zuwa Tripoli a ranar 20 ga Yuli tare da wani abokinsu da ba a bayyana sunansa ba kafin faruwar lamarin.

    10. Wani mummunan hatsari ya auku a ranar Lahadi lokacin da wani motar haya mai ɗauke da fasinjoji ta fada cikin rafin Namnai a ƙaramar hukumar Gassol ta jihar Taraba. Wannan ya bayyana ne a wani rubutu da wani masani kan tsaro, Zagazola Makama, ya wallafa a shafinsa na X. Ya bayyana cewa motar, mai ɗauke da tambarin Adamawa Express, ta yi ƙoƙarin ketare wata gada da ta ruguje kafin afkuwar hatsarin.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 13, Aug. 2025

    Takaitattun Labaran Safiyar Yau Laraba 13, Aug. 2025

    Labaran Najeriya A Yau – 13 ga Agusta, 2025

    1. Fursunoni 16 sun tsere daga gidan gyaran hali na Keffi a jihar Nasarawa bayan kai hari kan jami’an NCoS, inda jami’ai 5 suka jikkata.

    2. Gwamnan Anambra, Charles Soludo, ya ce ba shi da nadama kan hadin gwiwarsa da Shugaba Bola Tinubu duk da bambancin jam’iyyu, yana mai cewa suna da tsawon dangantaka ta shekaru 20.

    3. EFCC ta ce tana aiki ba tare da son rai ba, kuma tana bin doka ko da wanda ake zargi na cikin jam’iyyar mulki ne ko na adawa.

    4. Kamfanin Dangote Refinery ya rage farashin PMS a matakin gonar ajiya da Naira 30, kuma hakan ya fara aiki nan take.

    5. Sojojin Operation Hadin Kai sun kashe ‘yan Boko Haram da dama bayan sun kasa kai harin bam a hanyar Maiduguri-Kareto-Damasak, Jihar Borno.

    6. EFCC ta bayar da beli ga Aminu Tambuwal, tsohon gwamnan Sokoto, bayan tambayarsa kan zargin cire Naira biliyan 189 ba bisa ka’ida ba.

    7. Hatsari ya kashe mutane 5 a Ogun bayan tsere na mota da aka yi bisa caca ta N30,000, ciki har da matasa 3 da ake zargin ‘yan Yahoo ne da mazauna gari 2.

    8. ‘Yan sanda a Ogun sun kama mutane 2 da aka samu da kawunan mutane 3 a yankin Ijebu, kuma an fara gurfanar da su a kotu.

    9. Rukunin jam’iyyar Labour na Julius Abure ya gargadi INEC da kada ta cire tambarin jam’iyyar a zaben rani na 16 ga watan Agusta.

    10. ‘Yan sanda a Bauchi sun kama dalibai 48 na Federal Polytechnic Bauchi bayan zanga-zangar da ta hada da toshe hanya, kona tayoyi, jifan motoci, da fasa shaguna.

  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 12, Aug. 2025

    Labaran Najeriya Na Yau – 12 ga Agusta, 2025

    1. EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sokoto, Aminu Tambuwal a ranar Litinin don bincike kan zargin cire kudi har Naira biliyan 189 ba bisa ka’ida ba a lokacin gwamnatinsa.

    2. Hukumar Kwastam ta kama kwantena 16 dauke da kaya haram, ciki har da bindigogi, harsasai, kayan soji da miyagun kwayoyi, kimanin darajar Naira biliyan 10, a tashar jiragen ruwa ta Apapa, Lagos.

    3. An gurfanar da mutum 5 da ake zargi da kai hari a cocin Katolika na St. Francis, Owo, Jihar Ondo a 2022, a gaban kotun tarayya a Abuja.

    4. ’Yan bindiga sun kashe mutane 3 a Yelewata, Jihar Benue, yayin da Boko Haram suka kai hari kan sansanin soja a Borno, suka kashe sojoji 2.

    5. Peter Obi ya ce talauci da yunwa a Najeriya ba wai kididdiga kawai ba ne, illa ce ta gaske da ke shafar miliyoyin ‘yan kasa.

    6. An tura wata fasinja mace mai suna Comfort Bob zuwa gidan yari na Kirikiri bayan zargin tada tarzoma a jirgin Ibom Air da kuma fada da jami’an tsaro a filin jirgin sama na Lagos.

    7. Gwamnatin Tarayya ta fara daukar sabbin sakatarorin dindindin 5, 3 daga cikinsu za su jagoranci sabbin ma’aikatun da aka kafa.

    8. Gwamnatin Ogun ta rufe kadarorin Otunba Gbenga Daniel, tsohon gwamna kuma sanata, ciki har da otal-otal da Asoludero Court a Sagamu.

    9. Mataimakin kocin Shooting Stars, Akin Olowokere, ya rasu bayan faduwa a safe yayin aiki a ranar Litinin.

    10. ’Yan sanda a Lagos sun kama mutum 68 cikin wata guda kan laifuka kamar fashi da makami, garkuwa da mutane, da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.