Close Menu
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp
Twins Empire News
Demo
  • Gida
  • Labarai
  • Wasanni
  • Nishadi
  • Siyasa
  • Bidiyo
  • Game damu
  • Tuntubemu
Twins Empire News
Home»Labarai»Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 18, Agusta. 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 18, Agusta. 2026

By Ahmad Habib IbrahimAgusta 18, 2026No Comments2 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Reddit Telegram Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email
Demo
    1. Farashin kayayyaki ya ragu zuwa 15.43% a Najeriya
      Hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya ta ragu zuwa kashi 15.43 cikin 100 a watan Yuli 2026. Sai dai farashin kayan abinci ya sake fuskantar matsin lamba, kamar yadda rahoton NBS ya bayyana.
    2. Kakakin Majalisar Dokokin Edo ya yi murabus
      Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Edo, Blessing Agbebaku, ya yi murabus daga mukaminsa yayin da ake rade-radin cewa ‘yan majalisar na shirin tsige shi.
    3. An kama mutumin da ake zargi da kashe mahaifiyarsa
      Rundunar ‘yan sandan Ondo ta kama Samuel Akoade bisa zargin kashe mahaifiyarsa da adda a Ore, karamar hukumar Odigbo ta jihar.
    4. NDLEA ta lalata gonakin wiwi a Edo
      Hukumar NDLEA ta lalata gonakin tabar wiwi guda biyu masu nauyin kilogiram 4,628.9 tare da kama mutane 10 da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi.
    5. ‘Yan sanda sun tabbatar da tsaro gabanin zaben 2027
      Mataimakin Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Zone 2, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa rundunar ‘yan sanda ta shirya tsaf domin tabbatar da tsaro yayin zaben 2027.
    6. Naira ta kara daraja a kan dala
      Naira ta samu karin daraja da ₦8.07 a kan dalar Amurka a kasuwar canjin kudaden waje ta hukuma, inda ta rufe a kan ₦1,349.53 kan dala guda.
    7. Fiye da malamai 200 sun bar Jami’ar KASU
      Kungiyar ASUU ta Jami’ar Jihar Kaduna ta nuna damuwa kan barin aiki da sama da malamai 200, ciki har da farfesoshi, sakamakon rashin kyawun yanayin aiki da rashin aiwatar da yarjejeniyar ASUU da Gwamnatin Tarayya.
    8. Almajirai hudu sun mutu a Kano
      Akalla almajirai hudu sun mutu a Kano bayan cin abincin da ake zargin ya gurɓata. Kungiyar Tsangaya Media Network ce ta tabbatar da faruwar lamarin.
    9. Yawan motocin Air Peace da ‘yan sanda suka kwace ya koma biyar
      Motocin Air Peace da ‘yan sanda suka kwace domin gudanar da bincike bayan rikicin rufe titin saukar jiragen sama na Lagos sun karu daga uku zuwa biyar.
    10. Ma’aikatan Osun sun yi gangamin murnar nasarar Adeleke
      Ma’aikatan Jihar Osun sun gudanar da gangami a Sakatariyar Jihar da ke Abere, Osogbo, domin murnar nasarar Gwamna Ademola Adeleke, suna mai danganta nasarar da manufofinsa na jin dadin ma’aikata da ‘yan fansho.

Demo
Labaran Safiyar Yau
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Ahmad Habib Ibrahim
  • Website

Related Posts

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Juma’a 14, Agusta. 2026

Agusta 14, 2026

Me Ya Sa Muka Shirya Juyin Mulki a Kan Tinubu? – Kanal Ma’aji

Agusta 10, 2026

Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 30, Yuli. 2026

Yuli 30, 2026

Comments are closed.

Twins Empire Youtube
Wallafar Yanzu
  • Me Ya Sa Mutum Lake Aiki Tukuru Amma Har Yanzu Yake Cikin Talauci?
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Talata 18, Agusta. 2026
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Juma’a 14, Agusta. 2026
  • Me Ya Sa Muka Shirya Juyin Mulki a Kan Tinubu? – Kanal Ma’aji
  • Takaitattun Labaran Safiyar Yau Alhamis 30, Yuli. 2026
Nasara
Tsari
© 2026. Designed by Syntape Soultions.
  • Labarai
  • Nishadi
  • Wasanni
  • Contact Us

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.