EFCC ta ce shugabannin fansho na karkatar da kuɗaɗen jama’a a Najeriya

Shugaban hukumar EFCC Abdulrasheed Bawa ya ce shugabannin kamfanonin fansho na karkatar da bilyoyin kudaden mutane a Najeriya.

Ya shaida hakan ne a taron kwanaki biyu da ya ke halartar kan kawar da rashawa a tara kuɗaɗen fansho a Najeriya.

Bawa ya ce EFCC da ke yaƙar rashawa tana sane da irin aika-aika da ake aikatawa da kuɗaɗen fanshon mutane.

A cewarsa bincikensu ya nuna musu yada ake tafka rashawa a fanin fansho wanda hakan abin kunya ne ga kasa.

Ya kuma shaida cewa gwamnati na duba batun domin ganin ta samar da mafita da hukunta masu tauye hakkin mutane.