X

Tinubu ya zaɓi Kashim Shettima a matsayin mataimaki

Ɗan takarar shugaban Najeriya ƙarƙashin Jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu ya zaɓi tsohon gwamnan Borno Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a takarar shugaban ƙasa.

Tinubun ya bayyana haka ne ga ƴan jarida a garin Daura yayin wata ziyarar barka da Sallah da ya kai wa Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

Tinubun ya bayyana cewa duk da bai tattauna wannan batu da Kashim Shettima ba amma ga shi ya bayyana wa ƴan jarida.

Kashim Shettima dai a halin yanzu shi ne Sanata mai wakiltar yankin tsakiya na Jihar Borno.

Haka kuma Shettima ya bayar da muhimmiyar gudunmawa a yaƙin neman zaɓen Tinubu a lokacin zaɓen fitar da gwani na Jam’iyyar APC.

Categories: Labarai
twinsem2:
X

Headline

You can control the ways in which we improve and personalize your experience. Please choose whether you wish to allow the following:

Privacy Settings