Kotun ɗaukaka ƙara a Botswana ta tabbatar da hukuncin shekarar 2019 da ya halatta maɗigo da luwaɗi a kasar.
Alƙalai biyar na kotun sun yanke hukunci baki ɗaya cewa haramta auren jinsi ɗaya ya saɓa wa kundin tsarin mulki na ƴancin ƴan maɗigo da luwaɗi,
A shekarar 2019,babbar kotun ƙasar ta yi watsi da dokar da ta ce ta saɓawa kundin tsarin mulki wacce ta shafi ɗaurin shekara bakwai ga waɗanda aka kama masu alakar jinsi ɗaya.
Kotun ta ce ana cutar da ɗan Adam ne idan aka mayar da wasu tsiraru saniyar ware.
Amma gwamnatin ƙasar ta ɗaukaka ƙara inda ta ce ƴan ƙasar da dama ba su amince da hukuncin ba na shekarar 2019.
Ƙasashen Afrika da dama sun kyamaci auren jinsi ɗaya.